Mujallar FIM - March 2002

54
paste cover here

Transcript of Mujallar FIM - March 2002

Page 1: Mujallar FIM - March 2002

Fim, Maris 2002

paste cover here

Page 2: Mujallar FIM - March 2002

Fim, Maris 2002

Kumurci: Ya more matashafi na 19

Ligidi bai haukace ba---------------------------------------------------------------Ina masu rade-radin wai Ligidi ya tabu sakamakonhadarin mota a hanyar Kano? Ashe ku ne kuka‘haukata’ shi din!shafi na 16

’Yan fim sun je walimar Rabi---------------------------------------------------------------Ya aka yi wannan abin kunya? A ce ’yan fim su kihalartr durin auren Rabi Mustpha amma a gan su agun walima?shafi na 30

Gobara daga kogi a fagen fimna Jos!---------------------------------------------------------------’Yan fim na Filato sun yi wa kungiyarsu garambawul,amma har yanzu rikicin cikinta bai kare ba.shafi na 32

Fataken dare ... da rana tsaka---------------------------------------------------------------Barayi sun yi wa furodusa karkaf, kuma suka washegidan mawallafin mujallar Fimshafi na 34

’Yan Kaduna abin tausai!---------------------------------------------------------------A garinsu dirama ta soma yin tasiri a Arewa; yanzuko an maida su butal. Me ya sa?shafi na 42

Zauren intanet akwai zance---------------------------------------------------------------Jama’a daga sassa daban-daban na duniya sunatattaunawa a kan harkarfim na Hausashafi na 48

’Yan fim sun yi selula---------------------------------------------------------------Gogan naku, Malam Zurke, ya ga ’yan fim da damada ‘GSM.’ Yaushe zai yi tasa?shafi na 52

Mu Leka Mu Gani - shafi na 2Rayuwarmu - shafi na 5Wasiku - shafi na 6

Ku Tambaye Su - shafin 14Abokanmu - shafi na 15Kacici-kacici - shafi na 18

Hollywood - shafi na 39Zauren Intanet - shafi na 48Malam Zurke - shafi na 52

ANGO DA AMARYA?: Aliyu Abdullahi Gusau da Asiya Mustaphashafi na 27

Ta 27 * Maris 2002

1

RAHOTON MUSAMMAN: Dalilin hana kallon sinima a Zamfarashafi na 37

Page 3: Mujallar FIM - March 2002

Fim, Maris 20022

GASKIYAR masu iya magana da suka ce shekara kwanace, kuma tafiya sannu-sannu kwana nesa. O, wai harmun shekara uku da fara mujallar Fim! A gaskiya,

ban fahimci haka ba sai da wani mai karatunmu ya bugo wayaya ce yana taya mu murnar cika shekara uku. Da farko na yizaton ko dai yana nufin shekara biyu, amma sai na tuna ashea bara ne muka cika shekara biyu. To, tunda ga watan Marisya zo, kuma an fara buga Fim ne a cikin Maris 1999, lallaimun shekara uku kenan. Shin mu yi bikin murna ko kuwamu yi addu’ar Allah ya }ara agaza mana? A ganina, dukkansuya dace mu yi. To, ita addu’a ita ce farkon abin yi, kuma dama kullum a cikinta muke; shi ko biki, wannan sai mun shirya.

Shin me muka yi a cikin shekaru uku? Wa]anne nasarorimuka cimma mawa? Kuma wa]anne }udurori ne muka kasasamun nasara a kansu? Wa]annan tambayoyin sun ri}a ratsamani kai bayan waccan waya da mai karatunmu masoyinmuya yi mani. A kansu kuwa nake son yin tsokaci a nan.

Idan mai karatun wannan shafin ya dubi dukkan kwafenwannan mujallar na baya, zai iya fahimtar yawan aikin damuka yi tun daga farko har zuwa yau ]in nan. Kai da ganinwannan jerin ka san ba wasan yara ne ya haifar da shi ba;aiki ne wurjanjan aka yi. Ko da kai ba}on karanta mujallarne, da kallon ]an tarin kwafen nan ka san irin labaran damuka ri}a bayarwa a game da ’yan fim na Hausa (koda yakemukan ta~o Indiya da Amerika a filayen ‘Bollywood’ da‘Hollywood,’ da kuma ‘Nigerian Films’ – na ’yan Kudu –jefi-jefi). Labaranmu ba su da bambanci ta wajen siga da irinlabaran da fitattun mujallu na duniya kan harkar fim sukanbayar, wato mujallu irin su Empire, Total Film, Stardust,Filmfare, Video, VCD Now, Showtime, da sauransu.Bambancinmu shi ne mu mukan yi la’akari da yaddaaddininmu ya tsara mana rayuwarmu ne, don haka akwailabarai wa]anda in ba domin addini da al’ada ba, to da bahaka za a ri}a ba da su ba. Yawancin labaranmu sukanfuskanci al}iblar yadda za a ha~aka shirin fim ne, ba adur}usar da shirin ba. Don haka za ka ga labarai ne ]auke datarihin ’yan fim, da hira da daraktoci da furodusoshi dasauransu, da labaran tarurruka, aure-aure, ha]urra, dabukukuwa. Akwai labarai da muka buga a kan sa~anin dakan faru a tsakanin ’yan fim (misali mutuwar auren Halima;sa-in-sar Saima da Halima; rikici a }ungiyar Janzaki; rikici akan fim ]in Wasila; sa-in-sar Ibro da Takari; bada}alarRu}ayya da Zahara’u, da shari’ar su Mandawari). A duklokacin da muke ba da wa]annan labaran mukan yi amfanida hankalinmu don ganin mun ba kowa ha}}insa ba tare damun yi }o}arin goyon bayan wani ba, ko da kuwa cikinmu]aya da shi.

Sai dai kash! akwai masu kallonmu a matsayin masu tononsilili. Wannan ba gaskiya ba ne ko ka]an, domin in da a ce zamu ri}a tona dukkan abin da muka sani yana faruwa a shirinfim, to tunda dai an daina kife }asa da babu shakka za a hanaharkar baki ]ayanta ko kuma mutane su tsani masu yin harkar.Yawanci, masu abin fa]i (kamar ’yan daudu da ’yan ma]igoda magulmata da manema mata) su ne suke cewa ’yanmujallar Fim ba su damu da komai ba sai tonon silili. A cikinshekaru uku ]in nan, tone-tonen da za a ce mun yi ba su kai

tare da IBRAHIM SHEMEMU LE}A MU GANIHar mun cika

shekara uku!ko cikin cokali ba na kogin abubuwan asshan da ake tafkawaa shirin fim. Kuma wani abu shi ne har yanzu yawancin masushirin fim jahilai ne ta fuskar wayewa; yawanci karatunsucikin cokali ne, kuma ba su zagaya }asa da duniya ba sukasan abin da ke faruwa; yawanci ba su ta~a saduwa da aikinjarida suka san muhimmancinsa a gare su ba, shi ya sa saiyanzu ne idonsu ke bu]ewa suna gane dawan garin. Ba sukaratun mujallu da littattafai ko kallon tashoshin talbijin,musamman wa]anda suka shafi sana’arsu. Babu mamaki, acikinsu }alilan ne suka san menene intanet har su mallaki i-mel; ko su ]in ma ba su cin moriyar intanet ]in sosai. A shirinfim na Hausa ne ]an fim zai ga wasi}a a mujalla game da shiko wani nasa (don ya yi gyara) amma ya ]auki takobi ya cezai kashe ’yan mujallar.

Kada in manta; Fim ce mujallar Hausa ta farko da ta shigaintanet, kuma ta zauna daram har ya zuwa yau. Shigarmuintanet ya sa mun shigar da batun shirin fim na Hausa a ciki;domin kuwa akwai ]imbin mutane a nahiyoyi daban-dabanda suke sanin me shirin fim namu na Hausa yake ciki ta hanyarkaranta mujallar a intanet. Kuma kyauta muke saka mujallarbaki ]ayanta don kurum ganin cewa wannan zai iya ciyar daharshen Hausa gaba kuma ya taimaka wa ha~akar adabinmu.Kuma ko banza dai mujallar ta taimaka wa mutane wajenkaratun Hausa, musamman a yanzu da ake }amfar ababenkarantawa na Hausa, sa’annan ta nisha]antar kuma ta ilimintar.Wani lokaci nakan yi tunani: misali a ce babu mujallar nan,yaya tunanin masu kallon finafinan Hausa zai kasance gameda wa]anda suke kallo da kuma ji-ta-ji-tar da kan cika }asa?

Mujallar Fim ba ta }age, kuma duk labaranta sai ta yi bincikekafin ta buga su. Wannan ma ya taimaka mana wajen samunkar~uwa a wurin ’yan fim da masu kallonsu. Na sha cewa inda an kafa mujallar nan domin sharri ne, to da yanzu tadur}ushe, tunda Allah ba azzalumin kowa ba ne.

Akwai wasu mujallun fim da aka ]age buga su, ba donsuna sharrri ba, sai don saboda tsarin gudanar da Fim da kumasadaukarwar ma’aikatanta sun bambanta da nasu. Abin ba}inciki ne mu a gare mu a ce abokanmu sun dakatar da bugamujallunsu, domin kuwa wannan ya rage wa adabin Hausatagomashi. Muna fatan za su gama gyara tsarinsu su dawofagen mu ci gaba da fafatawa, domin kuwa mun zama]uwaiwai dole a zauna da mu a shirin fim.

A }arshe, bari in yi ]an yi tsokaci a kan masu karatunmu. Agaskiya, masu karatunmu su ne suke ba mu }warin gwiwarda ya sa ba mu yin fargaba ko jin shakku a kan ci gaba dawannan aiki da muka sa a gaba. Masu karatunmu suna dajuriya kwatankwacin irin tamu, shi ya sa ba su gajiya wurinnuna mana }auna. Fim ta fara fitowa ne a kan N80, ta komaN100, ta dawo N120, yanzu kuma tana N150. Wannan yafaru saboda hauhawar farashin kayan masarufi a Nijeriya,wanda kuma ya nuna cewa mu a nan }asar ci-gaban mai ginarrijiya muke yi tun lokacin da Obasanjo ya hau mulki. Masukaratunmu sun jure wa wannan }uncin. To, muna godiya.Kuma mu ma a namu ~angaren mun }ara }aimi wajen tabbatarda cewa muna yi masu aiki da gasken gaske. Allah kuma yabar mu tare. Duk wannan sharhi ba yabon kai ba ne, don hakakada ku ce na yi jahilci!

A }arshen }arshe, zan rufe da bayyana cewa don Allah ’yanfim su ri}a rungumar al’amuran zamananci masu amfani irinsu intanet. Yanzu kamar dandalin ‘Finafinan Hausa’ ]in nan,abin kunya ne a ce masu kallo ka]ai ne suka zantuka a cikinsa.Ya kyautu ’yan fim su shiga ciki a yi tare da su, musammantunda Hausawa sun ce zamani riga ne. Wassalam.

Page 4: Mujallar FIM - March 2002

Fim, Maris 2002

3

MASU KARATUNMU ...

Dalilin dadewarwasikunku

CAN a watannin baya, mun ta~a gaya maku cewa mujallar Fim takan samuwasi}u daga wurin masu karatu kamar ruwan sama. To, daga wancan lokacinzuwa yanzu wannan ruwan saman ya }aru, ya ma zama ko dai ruwan kogi ko

kuma ruwan teku. Domin kuwa a kullum mujallar tana samun wasi}un da sun isasu cika shafukanta baki ]aya, ga shi kuwa shafukan da aka ware domin wasi}un,ta}aitattu ne (duk da haka shafukan sun zarce na yawancin mujallu wajen yawa,

saboda wata mujallar ma shafi biyu takan ba filin wasi}u, misali Showtime ta}asar Indiya).

Sakamakon wannan yawan na wasi}u, wakilinmu Aliyu Abdullahi Gora IIkullum cikin karanta wasi}u yake a ofishinmu na Kaduna. Wasu wasi}un suna

masa da]in karantawa saboda ko dai kyan rubutunsu ko kuma ma’anarsu. Wasuan bugo su da tafureta ko komfuta, wasu kuma za ka ga rubutun kamar ka sa

miya da gishiri ka ci don kyau. Irin wa]annan wasi}un sukan samu damar shigacikin mujallar da wuri. To amma akwai wani nau’in wasi}un, inda za ka ga

rubutu ba kai ba gindi. Wani mai rubutun, kila ]an koyo ne, kai ka ce a yau ne yafara halartar makarantar ya}i da jahilci; ga alama bai ma san me tafureta take

nufi ba ballantana komfuta. Irin wa]annan wasi}un suna da wuyar sha’ani,domin a }o}arin da Gora ke yi na fahimtar rubutun sai ma ya kasa gane ma’anar

da ke cikinsu. A }arshe ma in ba a yi sa’a ba sai ya wurga su a kwandon shara.Saboda haka zai kyautu masu rubuto mana wasi}u su ri}a yin rubutu mai

kyau, irin rubutun da zai ja ra’ayin mutum har ya so karanta su. Ina amfanin ba]iba rai? Ina amfanin ka sha wahalar aiko da wasi}ar da a }arshe za ta kasa samun

shiga? Wata hanyar da mai karatu zai iya samun biyan bu}ata shi ne ya aiko dawasi}arsa ta hanyar i-mel (‘e-mail’). Ita i-mel, ta hanyar intanet takan zo, kuma

za ta zo ne a bugaggarta (wato an gurza da injin, ba wai cikin maye ba!), donhaka mu a nan illa kawai mu sa ta a kan shafin mujalla. Tunda kuwa ba sai an

sake buga ta da tafureta ko komfuta ba, sai ta fito kafin wadda aka aiko ta gidanwaya. Kuma ma ita wasi}ar i-mel, ta fi saurin zuwa idan an aiko, domin ita ‘kar-

ta-kwana’ ce, sha-yanzu-magani-yanzu. Don haka sai a kula don Allah.

Fim ta yi sabon EditaIna farin cikin sanar da masu karatu cewa mujallar Fim ta yi sabon edita. Wannan

ko shi ne ASHAFA MURNAI BARKIYA. Ga duk makarancin mujallar, sunanAshafa ba ba}o ba ne, domin ya da]e tare da mujallar a matsayin wakili, da

mataimakin edita, kafin ya koma ya zama editan mujallar Bidiyo. Ko lokacin dayake Bidiyo, shi editan musamman ne a Fim. To, wasu al’amura na gyare-gyareda muke cikin yi, don }ara inganta mujallar, su suka sa Ashafa ya dawo Fim a

matsayin cikakken edita. Shi dai Ashafa, hazi}in marubuci ne kuma ]an jarida.Yana da digiri a fannin aikin jarida wanda ya samo daga Jami’ar Bayero, Kano. A

Kano, kusan kowane ]an fim ya san Ashafa saboda kutsawarsa da kuma iyahul]a da jama’a. Sakamakon haka ya sha za}ulo wa mujallar labarai wa]anda, in

da ba domin himmarsa ba, to da wata}ila mujallar ba za ta ta~a buga su ba.Ashafa bai da kasala ko ka]an, sa’annan idan ya samu labari ya rubuta shi, kai kace kai da ke karanta labarin a gabanka aka yi komai. Don haka dai muna kyautata

zaton cewa zaman Ashafa edita zai taimaka matu}a wajen inganta mujallar acikin watanni masu zuwa. In kana zaton ba ka ta~a gamuwa da shi a wani wuri

ba, ga hotonsa nan a sama ka duba. Kila ma ka gane shi.

I B R A H I M S H E M E

Ashafa

MAWALLAFI/BABBAN EDITAIbrahim Sheme

*DARAKTA

Alh. Garba Dangida*

EDITAAshafa Murnai Barkiya

*WAKILAI

Kano: Muhammed Nasir;Kaduna: Iro Mamman,Aliyu Abdullahi Gora II;

Katsina: Bashir Yahuza;Sokoto: Bashir Abusabe

Bauchi: Nazeeb S. IbrahimJos: Isma’ila M. Isma’ila

Gusau: Abubakar Maihoto*

MARUBUTA NA MUSAMMANDanjuma Katsina

Balaraba Ramat YakubuHalima Adamu YahayaShafi’u Magaji Usman

Abdullahi Ibrahim Doguwa*

KASUWANCIMary Isa ChonokoSadiya Abdu Rano

*HOTO

Bala Mohammed Bachirawa*

LAUYOYIMamman Nasir & Co.

----------------Mujallar FIM (ISSN 1595-7780)tana fitowa ne a kowane wata dagakamfanin Fim Publications, No.22, Zaria Road, Gya]i-Gya]i,Kano, Nijeriya. Ofishinmu aKaduna: S. 11, Ibrahim TaiwoRoad, saman asibitin ‘Ya’uMemorial,’ gefen Kasuwar Barci,Tudun Wada, Kaduna. A aiko dadukkan wasi}u zuwa ga MujallarFIM, P.O. Box 10784, Kano. Tel.:062-417347, 243112. Adireshinmuna E-mail:[email protected]. Ba ayarda a sarrafa kowane ~angare nawannan mujalla ba tare da izini arubuce daga mawallafanta ba. Maisha’awa zai iya karanta Fim kyautaa ko’ina a duniya ta hanyar Internetta wannan adireshin:www.kanoonline.comHa}}in mallaka (m) FimPublications

(ISSN 1595-7780)Jagorar Mujallun Hausa

Page 5: Mujallar FIM - March 2002

Fim, Maris 20024

IDAN ana maganar garin da ya ba da gagarumarumargudunmuwa wajen ha~akar wasan kwaikwayo a arewacinNijeriya, to dole a sa Kaduna a jerin farko. A nan ne aka

haifi dirama ta Hausa, wato tun daga shirin Baban Laraiwanda Adamu Halilu ya shirya. Kafa gidan talbijin a Kadunaya haifar da ’yan wasa wa]anda suka zama abin kwatance afagen wasan kwaikwayo. A Kaduna aka yi {asimu Yero,wanda har yanzu yana nan yana ba da gudunmawa a wannanfannin na fa]akarwa da nisha]antarwa.

Ban da talbijin, akwai rediyo, akwai kuma Cibiyar Al’adunGargajiya da ke Jami’ar Ahmadu Bello, ga kuma HukumarAl’adu ta Kaduna. Wa]annan duk matattaru ne na gwanayen’yan wasa. Cikin fitattu da suka yi fice akwai Usman BabaPategi (Samanja), Umaru [anjuma Katsina (Kasagi), RashidaBello, Tabature [ndume, A’ishatu Mahuta, Musa Moham-med Abdullahi, Ashiru Sani Bazanga, Yusuf Barau, TaniUmar, Tandu, Rabi’u Rikadawa, da sauransu da dama. Dukdaa haka, ga alama masu shirya finafinai a Kaduna ba su]auka cewa suna da wa]annan hazi}an ba. Wannan ya sa aduk lokacin da za su shirya fim sai su garzaya Kano su kwaso’yan wasa.

To, mun yi amfani da Kaduna ne a matsayin misali. Abinhaka yake a jihohin Sokoto, Zamfara, Katsina, Filato, Bauchi,Gombe, Yobe, Neja, da duk inda ake yin fim. Furodusoshisun tsaya kai da fata cewa idan babu ’yan Kano a fim ]in su,to ba su burge ba, kuma ba za su yi kasuwa ba. A nan, bamuna yi wa ’yan wasan Kano ba}in ciki ba ne. Mun sancewa su a wurinsu ci-gaba ne, kuma wannan ne yake }aramasu kwarjini a idon duniya. To amma ya kamata kowanefurodusa a duk inda yake ya ri}a sa kishin garinsu ko jiharsua zuci. Wannan zai }ara wa ’yan wasan jiharsu martaba harsu ma a san su a duniya. Zai }ara ha~aka harkar a jihar, tayadda a }arshe }asar Hausa baki ]ayanta ce za ta ci moriya.

Sanya ’yan wasa iri ]aya a kowane fim ya sa a yanzufinafinanmu sun kasance kamarsu ]aya; idan ka kalli fimguda ]aya shikenan ya ishe ka misali da yadda fim ]in Hausayake, domin dai duk wasan kusan iri ]aya suke yinsa. Ammaidan ka gwamutsa da ’yan wasan jiharku su ma za su iya fitoda wata siga ta wasa wadda ta bambanta da wadda aka sabagani. Dalili kuwa shi ne ’yan wasan Sakkwato sun bambantada na Kaduna ko Bauchi ta wajen furucinsu da ]abi’arsu.Dalili ma kenan da aka ri}a ha]a su [anwanzan da su[anhaki a wasannin talbijin na shekarun baya.

Mun san cewa furodusa yana tunanin kasuwa, wato yaddajarinsa zai fita idan ya shirya fim. An riga an ci zuciyarfurodusoshi da furofagandar cewa idan babu fitattun ’yanwasan Kano a fim, to ba zai yi kasuwa ba. Su ma furodusoshinKano hakan suka ]auka. Lallai akwai }anshin gaskiya awannan batu. To, amma ai za ka iya surkawa: idan ka saAbida ko Ru}ayya a matsayin jarumar fim ]in, to sai kasamu wani hazi}in matashi a nan garinku ka sa shi a jarumi;idan ka sa Ahmad S. Nuhu ko Alhassan Kwalle a jarumikuma, to sai ka ]auki wata hazi}ar budurwa a nan garinkuta fito a matsayin jaruma. Sa’annan ka gauraya sauran ’yanwasan da na Kano da na garinku. A}alla dai a fim akwaimanyan matsayin wasa guda shida, to sai ka raba: uku Kanouku garinku. Sam, ba mu goyi bayan saka ’yan gari ]aya suduka shida a fim ba.

Haka abin yake ta fuskar ba da umarni da ]aukar hotonbidiyo na fim. Ya kamata daga yanzu masu shirya finafinai a

Ha~aka shirin fim a jihohi wajen Kano

RA’AYIN MUJALLAR FIM

jihohin da suke wajen Kano su ri}a sanya daraktocin fim]insu a garinsu idan dai akwai gwanayen ba da umarni ajihar. Wannan zai taimaka wa masu ba da umarni na jiha suma su fito a san su har a ri}a kiransu a Kanon suna yin wasa.

Mun ga inda wannan tsarin ya yi amfani. Kuma sam, bamu nufin wai a daina sanya daraktocin Kano suna ba daumarni a wajen Kano, musamman ma tunda sana’a ce waddaza su iya zuwa ko da }asar waje ne su gudanar da ita susamo daloli. Manufarmu a nan ita ce a ha~aka shirin fim ajihohi, kuma muna ganin wannan tana ]aya daga cikinhanyoyin da za a bi a cimma nasara, a samu ha]in kai, arage }orafe-}orafe, kuma ma a rage kashe ku]i.

Sa’annan su kansu masu shirya fim na Kano, ya kamatasu ri}a ]auko ’yan wasan wasu jihohin suna sakawa afinafinansu. Su sani cewa idan sun yi fim a ko’ina ne akekallonsa, ba Kano ka]ai ba. Misali, idan Zik ne jarumin fim]inka, sai ka ]auko wata yarinya daga Sokoto ko Katsina suyi wasan tare da shi, idan an gama sai ta koma (kada kumata ma}ale a Kano ta }i komawa can, domin hakan zai maidaita ’yar wasan Kano kuma!). Idan kuma ka ga dama, za kaiya ]auko Abdullahi Korau daga Zariya ya zama maka mai]aukar hoton bidiyo, ko Waziri Zayyanu ya zama makadarakta.

Amma fa duk wannan ba zai yiwu ba sai an fitar da sonrai a harkar. [abi’ar nan ta tuwona-maina ce ka]ai za tahana a samu yadda ake so; wato halayyar nan ta yawancinfurodusoshi da daraktoci ta saka wasu ’yan wasa a kowanefim za su yi. Misali, akwai wani ofishin shirya fim a Kanowanda in za su yi fim tilas ne a ciki su sa Ciroki, Lubabatu,Biba, [andugaji, Fati Mohammed (kafin ta yi aure) dasauransu. Sa’annan darakta ]aya ka]ai yake yi musu aiki.Wannan ya taimaka wajen kashe kamfanin, har yayinsa yaragu, domin ko fim ]ari za su yi da wuya mai kallo ya gabambancin labarin, tunda dai komai irin wanda aka gani abaya ne. Irin wannan ma ta shafi wani darakta wanda a dukfim ]in da ya shirya sai ka ga su Ali Nuhu, [anmagori,Ahmad S. Nuhu, da sauransu a ciki. Mai ]aukar hotonsa]aya ne, haka mai tsara labarin fim, da sauransu.

Lokaci ya yi da su kansu ’yan wasa za su kar~i gaskiyarcewa ba dole ba ne darakta ko furodusan da ya sanya su afinafinai uku da suka gabata ya ci gaba da sanya su a dukkanfim ]in da zai yi. Su tsaya su ji idan sun dace da matsayinwasan da ake so a yi. Kada su damu furodusa da darakta daselling (wato kamun }afa). A ko’ina inda harkar fim ta cigaba (misali Indiya da Chaina da Amerika da Turai) hakaake yi. Ba wai mun ce ba a selling a can ba, amma dai ba irinwanda ake yi a }asar Hausa ba ne. Mu a nan matsalar ma ta}azanta ne saboda yanayin yadda ake yin fim ]in; sai ka ga]an wasa ya yi fim a}alla hamsin a shekara. A Indiya daAmerika, bai fi ]an wasa ya yi fim hu]u ko biyar a shekaraba, tunda akan ]auki lokaci mai tsawo ana yin fim ]aya;haka su ma daraktoci da furodusoshi. To, su da yake }arfeda }arfi ake ha]awa, fim ]in nan uku da ka yi sun ishe kacin abinci a tsawon shekarar.

Idan har ana so harkar fim na Hausa ta ci gaba ta wannan~angaren, to sai an yi gyara. Sanya fuskoki ]aya a kowanefim ba zai inganta fim ]in Hausa ba, sai ma dai ya kashe shi.Furodusoshin da ke sauran jihohi ya dace su }udiri aniyaryin gyara tun daga garinsu, su kuma na Kano sai su maramasu baya.

Page 6: Mujallar FIM - March 2002

Fim, Maris 2002

Iya girki na }ara dan}onsoyayyar ma’aurata daga

BALARABARAMAT YAKUBU

2. Iya Girki

GIRKI shi ne mace. Ta hanyar baki a kan sami kan kowane namiji, komai taurin kansa kuwa. Duk matarda ba ta iya girki ba, to ba mace ba ce, domin ita da

babu ]aya suke. Shi namiji yaro ne, kamar yadda za ki baiwa ]anki nono ya sha har ma in yana hannunki ya ri}a }wiyarzuwa hannun wani, to haka namiji yake}wiyar zuwa gurin wata in dai kuma za kiba shi abinci mai da]i kuma mai tsafta,gurin da zai ci abincin a gyara. Ke dai kiba shi abincin a tsaftace. Kuma a lokacinda yake son ci, kuma abin da ya ce son ci,da kin burge. Sai yadda kika ce, kuma abinda kike so shi za ki samu a gurinsa. Donba zai je otel ba, ba zai yi sha’awar tsire atiti ba tunda kin iya gasawa, balle kazar datake a titi bayan kin iya sarrafa ta a ]akingirkinki mai tsafta. Kuma duk abin da zaki ce a kawo, a guje zai shigo da shi gida,don ya san ba zai yi asara ba. Ko da cinabinci ya kama shi dole a wajen ba zai ta~ayin gyatsa ba sai ya dawo ya ]ora naki akai. Kin ga kin }ulla sabuwar soyayya!

3. Wata kuma in tana da tsaftar da iyagirki, sai ka ga ba ta iya magana ba, ba tasan abin da za ta gaya masa ya ji da]i baballe kuma ta san amsar maganar da za tamayar masa in ya yi mata magana.

A wani lokaci ma kafin ya karya kumallo sai ka ji tadan}ara masa maganar da za ta sa ya ha}ura da cin abincinya bar mata gidan da wuri, ta sa shi ya fita waje ya nemi abinda zai ci, ko ya je ofis ya sa masinja ya sayo masa abincinsayarwa ya zauna ya ci dole don ba yadda zai yi. In ma’aikacine ko ]an kasuwa, haka zai yini yana ba}in cikin maganar,dole yamma ta yi ya dawo gida; don ba inda za shi da ya

A WATAN GOBE:Malama Hauwa’u, zan yi tsokaci a kan wannan

al’amarin na kishi, insha Allah.

5

‘Wata ta san tafa]i ba da]i,

amma ]anyenkai ba zai bar tata rarrashe shi

ba, sai ta nemi ta}ara kwa~a

masa wata...’

wuce gidansa. Wata ta santa fa]i ba da]i, amma]anyen kai ba zai bar ta tararrashe shi ba, sai ta nemita }ara kwa~a masa wata.

W a n ihar ya} a r ifushinsaya huce.I r i nwannanm a t a nza ka gab akasafaimazansukan yihira dasu ba,domin gudun ~acin rai. In har zai ba taku]in cefane, to Allah-Allah yake ya barmata gidan don kada maganar ta yi tsawoa sami damar kwa~a masa.

4. Duk wacce ba ta da hankali, to saidai a yi fatiha a tashi, domin ba ta damagani ban da Allah. Domin kowane irinabin da muka lissafa a baya to tana da shi,

don haka komai kan iya faruwa da ita, kuma za ta iya yinkomai. Abin da duk ta yi kuma ba ta san ta yi ba. Wanda yaha]u da ita ya san an yi asara ne kawai. Kuma in an yi mataba ta san an yi ba. Maganinta kawai addu’a. Amma duk~angaren ~acin rai da za a duba, to tana da hannu a ciki.

Mu ha]u a watan gobe.

Zuwa Ga Anti Balaraba,

BAYAN gaisuwa da fatan alheri. Anti, yaya }o}ari?Yaya kuma aka ji da jama’a? Allah dai ya }ara juriya,

amin.Dalilin wannan wasi}a tawa shi ne ina so Anti ta yi wa

irin matan nan masu mugun zafin kishi nasiha, dagawa]anda suke gidan mijinsu har na waje. Sannan ki nunamasu irin kishin da ya ya dace su yi, wato irin wandaaddinin Musulunci ya yarda da shi.

Domin na fuskanci yawa-yawan mata ba su san irinkishin da ya dace su yi ba, sai dai da ka ta~a su su ce kishikumallon mata, ko su ce matan Annabi ma sun yi kishi. Tomatan Annabi ba kishin jahilci suka yi irin wanda matanyanzu suke yi ba. Saboda abin dubawa a nan, Anti, sai kiga mace, musanman matar aure, ba ta da wani kishi illakawai kada mijinta ya yo mata kishiya, bayan ta mantacewa Allah (s.w.t.) da Manzonsa (s.a.w.) su ne suka bai waduk wani namiji damar auren mace daga ]aya har zuwahu]u. Kin ga kenan idan mata suka ce za su yi kishi dawannan, to ba makawa suna adawa ne da fa]ar Allah daManzonsa.

Amma sai ki ga wata mace ta gwammace ta zauna ita

ka]ai da mijinta tana murna ita wai ta tsare gida, ta hanakishiya shigowa, amma ba ta san meye mijin nata yake yia waje ba, ba ta sani ba neman matan banza yake? Kodayake wata ko ta sani tunda dai ba kishiya a gidanta, ta finono fari a wurinta. Amma ni ina ganin in har mace za tayi kishin, to ta yi a kan wadda ba halaliyar mijinta ba,wato karuwa (matar banza), amma ba a kan matar da zaiaura ba in dai so da kuma }aunarsa ne suka sa take kishinmijin nata domin ta sama masa tsira wurin Ubangiji.

Nan zan ta}aita sai wani lokaci. Ina ro}on AntiBalaraba Ramat ta daure kamar yadda ta saba ta yi wamata hu]uba a kan irin wannan matsala. Na gode.Hauwa’u Bello Mohammed (Mrs. AbbaAtiku Hotoro)Government Day Secodary School,P.M.B. 1035, Wukari,Jihar Taraba.

Ki ja hankalin masu mugun kishi

Page 7: Mujallar FIM - March 2002

Fim, Maris 2002

Muna maraba da wasi}un masukaratu. A tabbatar an sacikakken suna da adireshi,kuma a yi rubutu mai kyau. Ata}aita bayani.A aiko da sauri zuwa ga Edita,FIM, P.O. Box 10784, Kano.Tel.: 062-417347E-mail:[email protected]

Wasi}u

immediatepast

edition

6

INA KAUNAR RABI MUSTAPHAZUWA GA MUJALLAR FIM,

YABO da godiya suntabbata ga Allah

Ubangijin talikai. Gaisuwa gama’aikatan wannan mujallargaba ]ayansu da kuma fatanalheri gare ku, amin. Aha}i}anin gaskiya na sharekusan shekaru biyu ina karantawannan mujallar kuma munamatu}ar gamsuwa daayyukanku. Allah ya ba kuikon cika al}awarin da kuka yi,amin.

Bayan haka, don Allah inason ku mi}a gaisuwata gashaharrariyuar zabiyata, watoRabi Mustapha. Ha}i}a ni ina}aunarta }warai da gaske.Allah ya }ara mata basira,amin.Sabiu Musa (Japan)No. R. 1, Kano Street,Hayin Danmani, Rigasa, Kaduna.

JINJINA GA SARAUNIYA ABIDAZUWA GA MUJALLAR FIM,

NA kasance cikin walwala da farin ciki wanda ya zarce misatuwaa lokacin da na samu labarin sakamakon gasar finafinai na

2001, saboda kasancewar jarumata, wato Abida Mohammed, ita tamake sauran abokan gogayyarta da mummunan kaye, ta zamasarauniyar mata, kuma jarumar jarumai mata na 2001. Ina tayasarauniya Abida murna bisa wannan kyauta daga Allah .

A }arshe nake jinjina wa al}alan wannan gasa saboda nunabajintar da suka yi da kuma nuna }warewa wajen aikinsu. Da maan ce sharia sa~anin hankali, saboda haka nake kira ga duk wa]andaba su samu nasara ba da su yi ha}uri su ]au dangana sai kuma watashekarar. Ina gaishe da Abdulhamid da Nasiru, wato furodusoshinfim ]in {auna, da kuma Aminu Abba Shariff (Momo), jaruminjarumai maza, Ali Nuhu, sannan sarauniya Abida Mohammed tareda Hamza Sani [anzaki.Musa K. Abdulkadir,c/o Mastermind Entertainment, Jekadafari Quarters,Gombe.

...YA ZAN YI IN GAN TA?ZUWA GA MUJALLAR FIM,

NI dai mai son ganin tauraruwar ’yar wasan Hausa nan ce, watoAbida Mohammed. Ina son ganin dukkan wasanninta saboda

tana burge ni. To shi ne nake so in gan ta ido-da-ido. Don Allahyaya zan yi na gan ta?

Ina mi}a gaisuwata ga dukkan ’yan wasan Hausa.Maijidda Ahmad,

General Post Office, Nigerian Postal Service, Finance &Investment Div. Post, Kano.

Za ki iya ganin Abida idan kika je Sabon Titi, musamman ofishin‘Home Alone Production.’

...INA SON TARIHINTAZUWA GA MUJALLAR FIM,

INA son a ba ni tarihin Abida kuma ina son ganinta ina za ni nasamu ganinta? Don ina matu}ar }aunarta kamar yadda ya kamata.

Allah Ya }ara maku juriya, amin.Ado Mohammed,Dutse Motor Park, Dutse, Jihar Jigawa.

Mun sha ba da tarihin Abida a wannan mujallar. Ka dubafitowarmu na baya.

KU BA NI LAMBAR AHMAD S. NUHUZUWA GA MUJALLAR FIM,

INA son don Allah ku taimaka mani da lambar wayar Ahmed S.Nuhu idan yana da ita. Idan babu, to ina zan same shi idan na zo

Kano? Kuma ina son ku sanar da ni cewa wai hotunan da ake aikomaku da su }anana ne ko manya? Ina son ku mani bayani dominina son in zama abokin hur]arku.

Daga }arshe ina son Maijidda da Fati su daure su zauna gidanaure don Allah. Ina kuma gai da Fati Mohammed, AbidaMohammed, Ali Nuhu, Ahmed S. Nuhu, Hauwa Ali Dodo, MaijiddaAbdul}adir, da Shu’aibu Lawan Kumurci, Sani Mai Iska, SaniDanja, Tahir Fagge, Mandawari, Shehu Kano, Asiya Mohammed,Saima, da sauransu.Armaya’u Aminu,Kaita, Education Authority, P.O. Box 2020, Jihar Katsina.

Malam Armaya’u:Ahmad kamar sauran ’yan wasa masu lambar waya ba zai so mu

ba ’yan kallo lambarsa ba saboda gudun yawan buga masa wayadon a gaisa. Zai kyautu ka ga Ahmad da kanka ya ba ka lambar,domin kuwa yana da wayar selula ma. Maganar hoto kuma mun fison a aiko da mai ]an fa]i, ba }arami ba wato passport.

SHAWARA GA ’YAN WASAZUWA GA MUJALLAR FIM,

INA so in ba ’yan wasa shawarar su daina yi wa ’yan’uwansu ’ynwasa ba’a kanyadda Allah ya halicce su. Su sani cewa ba su suka

yi kansu ba.Bayan haka ga shawara kuma ga Abida Mohammed. Don Allah

ta daina girgiza jikinta in tana rawa saboda ba mutuncinta ba ne.Tana zubar wa da mata mutunci. Da fatan za ta yi amfani da wannanshawara.

Daga }arshe, ina mi}a gaisuwata ga gwanayena, irin su Aina’uAde, Tahir Fagge, Ibrahim Maishunku, Hajara Usman, Ishaq SidiIshaq, Balaraba Mohammed, da daraktan daraktoci Tijjani Ibraheem.Sakina Sani Gwarzo,No. 536, Dala Road, B.U.K. New Site, P.M.B. 3011, Kano.

GAISUWA GA JARUMAINAZUWA GA MUJALLAR FIM,

INA so in yi amfani da wannam dama in gai da jarumaina mazada mata. Ina so in fara da maza saboda a cikin Al}ur’ani Allah na

cewa maza na gaba da mata. Ina so ku isar da gaisuwa da fatanalheri ga Aminu Shariff (Momo, gwarzon shekara), Sani SK, IshaqSidi Ishaq, Ibrahim Maishunku, Sani Danja, Ahmad S. Nuhu daShu’aibu Lawan Kumurci. A mata kuma akwai Hauwa Ali Dodo,Aina’u Ade, Balaraba Mohammed, Aisha Musa, Abida, da zabiyarzabiyoyi Rabi Mustapha.Idris Abubakar

Page 8: Mujallar FIM - March 2002

Fim, Maris 2002

ND 15 Oyo Road, Unguwar Kaji Ward 2, Doka, Kaduna.

TAYA MUJALLAR FIM MURNAZUWA GA MUJALLAR FIM,

DA fatan wannan wasi}a tawa zata samu shiga. Ina son in yiamfani da wannan damar in nuna farin cikina da kuma taya

ku murnar cika shekara uku da kafuwa. Ina fatan Allah ya }aramuku jagora a kan }o}arin da kuke yi wajen buga wannan mujallarmai albarka.Bello Abdu-Qadir (Kankis),Funtua Textile Limited, P.O Box 64 Funtua, Jihar Katsina.

SABODA WASILA NAKE KALLON FIMZUWA GA MUJALLAR FIM,

INA ro}onku da ku sada wasi}ata zuwa ga Wasila Isma’il sabodaita ce musabbain samu ra’ayina na karanta mujallar Fim da kallon

finafinan Hausa. A kowane yanayi ta fito tana biyana.To ro}ona a rayuwa, Ubangiji Allah ya }ara wa Wasila ]aukaka

da rayuwa mai amfani duniya da lahira, amin summa amin.Tijjani Bashir,No. 29, Saminaka Road, Sabon Garin Tudun Wada,Kaduna.

GAISUWA GA ’YAN WASAZUWA GA MUJALLAR FIM,

INA son a mi}a min gaisuwa ta musamman ga abokanmu kumamasoyanmu kuma fittatun ’yan wasa kamar su Ali Nuhu, Ahmed

S. Nuhu, Shu’aibu Lawan (Kumurci), Abida Mohammed, daBalaraba Mohammed. Kuma ina taya Fati Mohammed murnaraurenta da ta yi. Ku huta lafiya.Sani Isma’il Dayawa JH,Jahun Unguwar Sarkin Gabas, No. 477 Toshi\on layiQuarters, Jahun, Jihar Jigawa.

HALIMAR DA MUKA SANI CE?ZUWA GA MUJALLAR FIM,

WANNAN tambaya ta da]e tana ]auran kai, tambayar kumaita ce: don Allah cikin marubutanku na musamman kukan

rubuta suna kamar haka: HALIMA ADAMU YAHAYA. Wai shinHalima da muka sani ce, wato sarauniyar finafinai ta 2000, ko kumawata ce daban? Ku huta lafiya.Yusuf Suleiman Musa,Dept. of Accountancy, University of Maiduguri, JiharBorno.

E, Halima Adamu Yahaya ce, wato ’yar wasan Hausa.

MUN GAJI DA ‘KASHI NA 2’ZUWA GA MUJALLAR FIM,

DON Allah ku ba ni fili domin na yi ]an ta}aitaccen bayani akan abin da na lura a game da masu shirin finafinan Hausa.

Wannan al’amari ko kuma na ce ciwo zai fi kyau na kira shi dasuna a Turance, ‘Part Two Syndrome’ – ‘ciwon kashi na biyu’. Zaiyi wahala a yanzu a sayi fim ]in Hausa ka gama kallonsa a cikinkaset ]aya. A ta}aice, idan mai kallo ya lura zai ga kwata-kwatagundarin fim ]in ba ya wuce awa ]aya tak, ragowar minti gomasha biyar zuwa minti talatin sai ka ga duk talla ne. To ba wai tallane ba a so ba; a’a mu dai abin da masu kallo suke so shi ne a ba sunisha]i daidai ku]insu tunda dai fim muka saya ba wai talla ba.

A ha}i}anin gaskiya za ka ga wani labari akwai bu}atar a yimasa kashi na 2 saboda tsawon labarin da muhimmacinsa, wanikuwa za ka ga kashi na ]ayansa ma kame-kame ne, amma sai a cenemi kashi na 2. Wani fim ]in kuma za ka ga labari ya }are a kashina ]aya amma don zalama ko don an ga fim ]in ya samu kar~uwasai ka ga can wasu sun shiryo kashi na 2. To babban abin haushi

ma a shi wannan ‘ciwon kashi na 2’ shi ne sai ka ga fim mai labarikyakkyawa, ingantacce da ma’ana, amma bai }are ba an ce a nemikashi na 2, sai ka yi ta zuwa kasuwa kana tambaya sai a ce bai fitoba. Wani ma sai kashi na ]ayan ya kusan shekara da fitowa sannanka ga kashi na 2 ya fito. Wani lokacin ma har sai ka manta dayanayin yadda kashi na ]ayan yake, sannan kashi na biyun ya fito.

Don Allah, don Annabi, kiran da zan yi wa masu shirya finafinanHausa shi ne, mu masu kallo mun san cewa shirin fim, musammana wannan zamani, yana da wahala. Amma abin da za ku yi la’akarida shi shi ne, ku daina lura da nawa za ku samu a kan fim, ku dingala’akari da cewa fa]akarwa kuke yi, duk kuwa mai wa’azi ba yanayi ba ne domin neman riba. Amma kuma a wani ~angare kuwa,kuna ha]a fa]arkarwar taku da nisha]arwa, shi ma ana mainisha]antarwa, ba burinsa ba ne ya tara ]imbin riba tunda burinsashi ne jama’a su gamsu da irin baiwar da Allah ya ba shi. DonAllah a kiyaye.Tijjani Musa Muhammad,MicroBiology/Parasitology Unit, Pathology Department,National Orthopaedic Hospital, Dala, P.M.B. 3087, Kano.

MASHAHAMA TANA BURGE NIZUWA GA MUJALLAR FIM,

SHIRYE-SHIRYENKU na }ayatarwa. Allah ya saka muku daalheri, domin mujallar Fim tana }ara sha’awar fim a wajen

al’umma.Ga gaisuwata nan zuwa ga Maryam Mohammed [anfulani

(Mashahama) domin tana burge ni da finafinanta. Allah ya }arataimakawa, amin.Hamisu Jafaru (Hamsal)Jahun, Tafida. Kofar Arewa, Tsigi Quarters, House No.149, Jahun, Jihar Jigawa.

MUJALLAR FIM KUN KYAUTAZUWA GA MUJALLAR FIM,

KARRAMAWAR da mujallar Fim ta yi wa maka]a da masuwa}ar finafinan Hausa ta dace }warai da gaske, kuma wannnan

zai }ara wa mujallar farin jini da ]aukaka a fa]in duniya. Idan harmujallar za ta karrama wasu a nan gaba, to ’yan wasa ya dace takarrama.

Daga }arshe, ina so in jinjina wa furodusa Musa Bamalli, daA’isha Isa Aliyu, da Ru}ayya Adam kan tsokacin da suka yi a kanmaganar da Ibrahim Mandawari ya yi a filin wasi}u a shirin MuSha}ata (part 2). Allah ya sa Malam Ibrahim Mandawari ya jinasihar kuma ya gamsu. Kuma ina gaida Fati Mohammed.Jamilu Sani, Shehu A.D., Mahmud Ibn Abubakar,Abubakar Mohd,Abubakar Gumi College, P.O. Box 679, Kaduna.

A BAR WULAKANTA JAMA’AZUWA GA MUJALLAR FIM,

ZAN yi amfani da wannan dama ina nuna ~acin raina ga irinwula}ancin da wasu ’yan wasa ke yi wa masu kallonsu. Irin

wa]annan ’yan wasan su sani fa cewa ]aukaka daga Allah take,sai wanda ya so zai ]aukaka. Don Allah ya ]aukaka mutum baikamata a ce yana wula}anta mutane ba. Ire-iren wasu daga cikinabubuwan da wa]annan ’yan wasa suke yi wa ’yan kallonsu masu}aunarsu, sun ha]a da share su idan sun yi musu magana, rashinkar~arsu hannu bibbiyu idan sun je neman su, da kuma rashinsaurararsu in sun yi musu waya. Wa]annan halaye idan aka bincikaaka yi nazari a kansu, za a ga cewa suna da babbar ala}a dawula}anci.

Ya ku ’yan wasa masu irin wa]annan halaye! Ku tuna fa, a cikinarba’una hadis, ku san }arshen hadisi na 32 wanda aka kar~o dagaAbi Huraira, a inda Manzon Allah (SWA) yake cewa: “Kowanne

7

Wasi}u

Page 9: Mujallar FIM - March 2002

Fim, Maris 2002

Musulmi ]an’uwan Musulmi ne. Kada ya zalunci ]an’uwansamusulmi, kada ya yi masa }arya, sannan kuma kada ya wula}antashi. Tsoron Allah a nan yake’ – (ya fa]i haka har sau uku yananuna }irjinsa na hannun hagu (zuciya) – ya ci gaba da cewa: ‘Yaishi sharri ga mutum wula}anta ]an’uwansa Musulmi.” Ya }arada cewa: ‘Duk Musulmi ga ]an’uwansa Musulmi, jininsa,dukiyarsa da mutuncinsa, haramun ne.” (Musulim ne ya ruwaito).Hassan Muhammad,No. 1 H-HRBDA Quarters, Management Staff Quarters,C.B.N. Road, Hotoro G.R.A., Kano. Tel 064-667241

MARTANI GA ANAS DAN MALIKIZUWA GA MUJALLAR FIM,

MUNA so mu yi amfani da wannan dama mu ba Anas [anMaliki amsa a kan kare Ishaq Sidi Ishaq da ya yi dangane da

maganar da Malam Isma’il Yusuf ya yi a mujallar Fim ta watanMayu 2001 shafi na 17, inda ya fa]i cewa Ishaq yana kakkamajikin ’yan mata, wanda haramun ne a addinin Musulunci.

To ai idan Malam Anas ya yi tunani, bai dace mutum yana aikatasa~o ba a ce mai a rufa masa asiri. Kuma mu a ganinmu mujallarFim ce hanya mafi sau}i domin sadarwa ga dukkan ’yan wasanfim. Don haka maganar Isma’il Yusuf tamkar nasiha ce da kumawa’azi ga Ishaq. Wata}ila bai da wata hanya mafi sau}i da zai iyasaduwa da ita sai ta hanyar mujallar Fim. Da fatan Anas [an Malikiya gamsu kuma Ishaq Sidi zai gyara.Abbas Abubakar, Aminu Abubakar, Fati Abubakar,Usman Abubakar (Abba)KY 12, Bima/Zango Road, Tudun Wada, Kaduna.

KU BA NI ADIRESHIN KABARAZUWA GA MUJALLAR FIM,

TARE da fatan an yi Sallah lafiya. Yaya aikin da kuke gudanarwa?Da fatan komai yana tafiya yadda ya kamata, Allah ya saka

muku da alherinsa, amin. Mu a nan Bauchi muna matu}ar yabawada nuna goyon baya kan yadda kuke gudanar da ayyukanku. Allahya bar mu tare don girman Ma’aiki.

Bayan haka wannan shi ne sa}ona na uku zuwa gare ku, narubutio wasi}a ta ta hanyar sadarwa ta i-mel domin neman saninadireshi jaruma Hadiza Moh’d Kabara. Ba don komai ba kuwa saidomin burge ni da take yi a finafinan da take fitowa. Saboda hakanake ro}on wannan mujallar mai farin jini ta taimake ni da adireshinda zan ri}a turo sa}o zuwa ga wannan ’yar wasa mai tashe, maifarin jini da kowa ke son wasanninta. Daga }arshe nake fatan za ashare mun hawayena. Ku huta lafiya.

Auwal Babangida Wunti,c/o Sulaiman Babayo, P.O. Box 350, [email protected]

Ba mu da adireshin Hadiza, amma idan ka yi inkiya da mu zamu ba ta wasi}arka hannu da hannu.

INA SON MUJALLAR FIMZUWA GA MUJALLAR FIM,

NA rubuto muku domin in shaida muku irin farin cikina gameda wannan aiki naku. Allah ya ja zamanin wannan mujalla.

Ina fatan za ku ci gaba da wannan namijin }o}ari na ilimantar daal’umma, ku da masu yin fim.

Ni dai ina tabbatar maku da cewa Allah ya sa mani tsananin sonfinafinan Hausa. Shi ya sa tun da na fara ganin wannan mujallar taFim, duk yadda za a yi in same ta sai na yi. Wannan ya sa duk watasai na kashe sama da N300 in bayar a sawo mini a Kano.Yushehu SalehSha’iskawa Quarters, Daura, Jihar Katsina.

KU FAHIMTAR DA NIZUWA GA MUJALLAR FIM,

NA rubuto muku domin in jinjina muku. Bayan haka, don Allahina son in yi tambaya game da Aleebaba Yakasai (‘Iyan-Tama

Multimedia’). Shin shi ne ya yi ki]in wa}o}in fim ]in Alaqa?Daga }arshe, ina mi}a gaisuwata ga dukkan ma’aikatan wannan

mujallar mai farin jini da kuma Musbahu M. Ahmed, Sadi SidiSharifai, Sani S.K., Momo, Mudassiru {asim, Ibro da Aleebaba.

Ku huta lafiya, Allah ya taimake mu baki ]aya.Jafaru AbdulsalamSha’iskawa Quarters, Daura, Jihar Katsina.

Aleebaba ya yi wasu ka]e-ka]e a Alaqa, amma wasunsu naIndiya ne aka ]auko aka sa.

A RIKA FASSARA FINAFINAIZUWA GA MUJALLAR FIM,

INA son in mi}a godiyata a gare ku dangane da irin }o}arin dakuke yi wurin aiwatar da aikinku da kuma biya wa masu karatu

bu}atarsu. Allah ya saka maku da alherinsa, amin.Ina so in sanar da masu harkar fim cewa ha}i}a suna yin }o}ari

da gaske kuma finafinansu suna kar~uwa a duniya duk da dai ba ajin yaren namu amma masu saurare suna amfana. Mutane da damasukan yi burin da a ce ana fassara fim ]in da Turanci ko Faransacida zai fi, kuma kasuwar finafinan za ta }ara fa]a]a.

Daga }arshe nake mi}a godiyata da kuma gaisuwa ga ’yan wasakamar Hajiya uwar gida sarautar mata Hauwa Ali Dodo, da Ibrahim

Wasi}u

Shin ka ga mujallar Fim a Intanet?A kowane wata mujallarku mai farin jini tana fitowa adandalin duniya na Intanet, ta yadda mutum zai iyakaranta ta a ko’ina yake a duniya – daga Amerikahar kasar Sin.Ka duba adireshin intanet nawww.kanoonline.coma cikin sashen ‘Publications’za ka ga mujallar har zuwa ta wannan watan damuke ciki.

In ko haka ne, me zai hana ka tallata hajarka a cikinmujallar, tunda dai a yau ita ce kadai hanya mafisauki da za ka tallata ta a duniya? Ka tuna, shiryafim ba tare da tallata shi ba kamar harara a duhu ne.Me zai hana ka sa tallarka a cikin FIM? Jagorar Mujallun Hausa

8

Page 10: Mujallar FIM - March 2002

Fim, Maris 2002

Mandawari, Bashir Bala, Sani Garba S.K. da Abida. Sai gaisuwaga mawa}anmu kamar su Musbahu M. Ahmad mai sanyaya zuciyada sautin wa}a, da Fati Abubakar, da Zuwaira da Sadi da MalamMudassir ]an gidan Alhaji {asim. Ku huta lafiya.Sabi’u Badamasi Dorayi,Ambassade Du Nigeria En Algerie, Tel 0021321 916389.

INA SON ABOTA DA HAFIZU BELLOZUWA GA SIR HAFIZU BELLO,

DALILIN rubuto maka wannan ’yar takarda tawa shi ne dominin shaida maka cewa ina son in zama abokinka, koda yake ka

girman nesa ba kusa ba, domin ina da shekaru 22 a bana.Sir, ina son finafinan da kai ma darakta matu}ar gaske. Duk

lokacin da na zo Kano insha Allah zan zo wurinka. Ranan na bugowaya ofis ]in Ishaq Sidi Ishaq, na tambayi wayar ofis ]in ka akace ba ka da waya. Ina son ka aiko man da hotonka ta wannanadireshi:Safiyanu Ibrahim,c/o Mani Ibrahim Musawa, General Hospital, Katsina,P.M.B. 2018, Katsina.

MANDAWARI, BAN YARDA BAZUWA GA SIR HAFIZU BELLO,

MUNA }ara muku godiya a bisa }o}arin da kuke yi mana naya]a mana labaran fim na kusa da na nesa.

Ina son in yi tsokaci a kan maganar da Ibrahim Mandawari ya yia wannan mujalla ta watan nuwabba inda yake cewa wai duk acikin ’yan fim ba a ta~a samun mai kyau irin Balaraba Mohammedba. Ya Mandawari zai fa]i wannan magana? Ko ya manta da irinsu Fati Mohammed ne? Ko an ci moriyar ganga ake son a yadakwaurenta? Sai dai ka ce ka fi son Balaraba ]in, amma ba ta fikowa ba. Sa}on gaisuwa ga sarauniyar ’yan fim Abida Mohammed,Ibro, Ali Nuhu da kuma Kumurci.Hadiza Abubakar,No. 1, behind Post Office, Katsina.

RUKAYYA DA ZAHRA’U KU SASANTAZUWA GA MUJALLAR FIM,

NA rubuto muku wannan wasi}a ne domin in jinjina muku nabisa irin wannan namijin aikin da kuke gabatar mana. Ha}i}a

ko ba komai kun cancanci yabo.Zan kasance mai matu}ar farin ciki in har na samu fili a cikin

wannan hamsha}iyar mujalla, don in isar da sa}ona ga kyawawanjarumaina guda biyu, Rukayya Umar Santa da kuma Zahara’uShata dangane da sa~anin da ke tsakaninsu. Don Allah su kamakansu. Domin ina shaida musu cewa suna da }ima }warai da gaskea idon jama’a. Yawan tone-tonen asirinsu ko shakka babu zai iyashafarsu. Sannan ya kamata su kare mutuncin sana’arsu. Domin inhar irin wannan tana faruwa, to ha}i}a zai iya shafar sana’ar fim.

Daga }arshe ina mi}a gaisuwa ta musamma ga Shehu Kano daantina Hajara Usman da Alhassan Kwalle da kuma Bashir Nayaya.Danjuma Abdullahi Disina,Dept. Primary Heath Care, Shira L.G.A., Jihar Bauchi.

KUNA BA NI MAMAKIZUWA GA MUJALLAR FIM,

BA abin da zan ce wa mujallar Fim sai Allah ya }ara ]aukaka taya kuma }ara mata farin jini. Mujallar Fim tana burge ni fiye

da yadda ake tsammani kuma na gamsu da tsarin labarunta, dayawan shafuka, da kuma yadda ma’aikatanta suke aiki. Ni ina zamaa garin Baga cikin }arama hukumar Kukawa da ke arewacin JiharBorno, amma sai na sami mujallar a kowane wata, sa~anin sauranmujallu da sunansu kawai nake ji. Wannan abin yabawa ne, cewaga mujallar Hausa muna ri}e da ita a hannunmu. Da ma Hausawasun ce da rashin uwa akan yi uwar]aki; saboda rashin namu, shi yasa muke karanta mujallun Kudu masu cike da labaran batsa da

Wasi}ukuma lalata tarbiyyarmu.

A }arshe ina gaisuwa ga Ibrahim Sheme, Tahir Fagge, HadizaKabara, Hauwa Ali Dodo da kuma sarauniyar ’yan wasan Sokoto,wato Sa’adiyya Abubakar Tambuwal.Abubakar Adam,P.H.C. Dept., Kukawa LG.A., Jihar Borno.

MAI ISKA KA ZAUNA DA MACE DAYAZUWA GA MUJALLAR FIM,

INA so ku ba ni ]an fili a cikin mujallarku mai farin jini domin inbai wa wani ]an wasa, Sani Musa Mai Iska, shawara game da

yadda yake tafiyar da rayuwar aurensa a Musulunci.Abin mamaki ne da Sani ya auri Talatu sai daga baya muka ji

wai ya saki uwargidan Talatu; sai mutane suka yi ta cewa wai Talatuce ta kore ta. Ana nan ana nan sai Allah a cikin ikonsa ya auri FatiMohammed. Ba ta fi wata uku cikakku ba sai muka ji ya saki Talatu.Mutane sai cewa suke wai Fati ce ta kore ta; sai ga shi a mujallarFim Talatu ’yar halak ta fito ta yi bayani cewa duk wanda ya ceFati ce ta kore ta, ya ]auki alhakin Fatin.

To, Sani, yanzu dai mun gane laifinka ne. Ba za ka iya zama damata biyu ba bare uku ko hu]u. Saboda haka ne nake ba ka shawaraa kan ka ha}ura da mace ]aya domin ba za ka iya zama da matabiyu ba. Annabi (s.a.w.) ya ce mutum ya auri mata daga ]aya zuwahu]u, amma in zai yi adalci; in ba zai yi adalci ba to ya auri ]aya,]ayar ma in ba zai yi mata adalci ba, to ya auri kuyanga ko baiwa.To, za~i ya rage naka!

Daga }arshe ina mi}a gaisuwata ga mawallafin mujalla mai farinjini Ibrahim Sheme, sai ’yan wasa kamar Tahir Fagge, Ali Nuhu,Biba, Ahmad S. Nuhu, da sauransu.Hauwa Muhammad (Anti Kulu),No. 1, Planners Street, NNDC Quarters, Sharada, BUKRoad, Kano.

INA SO TIJJANI YA GWADA NIZUWA GA MUJALLAR FIM,

DON Allah ina so ku taimaka ku ha]a ni da shahararren daraktannan Tijjani Ibraheem domin ya gwada ni a cikin wani fim

]insa, kasancewata mai sha’awar finafinai tun daga farkonbun}asarsu har ya zuwa yanzu. A gaskiya na da]e ina sha’awarfitowa a cikin fim, to amma ban sami hali ba. To, ina ro}onku daku taimaka mani domin ganin na cimma burina.

Kuma don Allah ku isar mani da gaisuwata a wajen gwarzonakuma masoyina, wato takwarana Ali Nuhu; sai masoyiyata Aina’uAde (Laila) da Ishaq Sidi Ishaq, da dukkan ’yan wasa. Na gode.Ali Sani Sheme (Gambo),c/o Sani Abubakar, First Bank of Nigeria Plc., No. 1,Crescent Road, P.M.B. 1006, Zaria, Jihar Kaduna.

Malam Ali, idan ka zo Kano za ka ishe Tijjani a ofishinsa da ke‘Fasaha Films,’ Zoo Road (duk ]an fim da ka tambaya zai iya gayamaka wurin), daga nan shi daraktan zai gaya maka yadda yake yiyana ]aukar ’yan wasa. Allah ba da sa’a. Edita.

UZURI YA YI KYAU, TO AMMA...ZUWA GA MUJALLAR FIM,

MA{ASUDIN yin wannan wasi}ar shi ne domin in yi tsokaciga mashahurin kamfanin shirin fim na ‘Ibrahimawa

Production’ game da fim ]insu mai suna Uzuri. Alal ha}i}a shirinya yi matu}ar kyau, a yadda aka tsara labarin da kuma tsara maganarda ke cikinsa, a gaskiya na ji da]in kallonsa }warai da gaske.To, sai dai kasancewar Ishaq a matsayin jarumin shirin ya rage wafim ]in armashi. Domin kuwa fuskar da ba ta yi fice ba kumaba}uwar fuska za ta fi dacewa da matsayin. Saboda shiri ne maitsotsa zuciya da tausayi. Don haka duk wanda ya kalli irin su Ba’asi,

9

Page 11: Mujallar FIM - March 2002

Fim, Maris 2002

Wasi}u

10

to tausayin zai ragu gare shi ko ma bai jin tausayi sam-sam. To shiya sa na ce haka.

Don Allah ina son a mi}a mani gaisuwa ga Ishaq Sidi Ishaq,Ibrahim Mandawari, A’isha [ankano, Saratu Gi]a]o, ZulkifiluMuhammad, Hafsatu Shara]a, Hadiza Kabara, da Wasila Isma’il.Ahmed Mustapha,Manchester Fans, No. 11, Nagwamatse Road, Sokoto.Tel.: 060-231072

KU RIKA BUGA WASIKUNAZUWA GA MUJALLAR FIM,

NA aiko da wata wasi}a inda ba da amsar gasar kacici-kacici ta12, amma ban ga an buga ta ba, kuma na ci amsar cewar “Saratu

Gi]a]o ce”. Don Allah edita ina son a yi man }o}arin buga minwasi}ata don in samu }arfin aiko maku da wasu da na tanadarmaku.Alh. Sabi’u K.K.,Nagwamatse Crescent, Sabon Gari, P.O. Box 160,Kontagora, Jihar Neja.

NA GA WASIKATA NA GODEZUWA GA MUJALLAR FIM,

NA yi farin ciki sosai da ganin takardata ta farko wadda na fararubuto maku ta fito. Allah ya }ara ba da }arfin gwiwa. Bayan

haka, ga wasu tambayoyina: Idan ina son in kasance cikin mutanewa]anda ke shirya finafinai, yaya zan yi? Na biyu, me ya sa ba kuda wakili a nan jiharmu ta Kabi?

Daga }arshe, idan akwai wani abu da kuke aiko wa masu hul]ada ku, ku aiko mani.

Ina gai da Balaraba Mohammed, Abida Mohammed, da Ru}ayyaDawayya. Kuma ga hotona nan ku buga.Cpl Mohammed Sani Kamba,Nigeria Police Force, Dakin-Gari Div., Suru LGA, JiharKebbi.

Zai kyautu ka sadu da wani ]an fim ya yi maka bayanin yadda zaka shiga harkar fim. Batun wakili, muna da shi a Sokoto, kuma shike kula da Kebbi, amma insha Allah nan gaba za mu yi wakili aKebbi kanta.

ALLAH YA ZAUNAR DA SU LAFIYAZUWA GA MUJALLAR FIM,

DALILIN rubuto maku wannan wasi}a shi ne domin na }aranuna jin da]in yadda kuke gudanar da aikinku cikin tsari.

Don Allah a }ara }o}ari fiye da yanzu. Allah ya taimake ku a kanma}iyanku, amin. Kuma don Allah a ri}a cika mana al}awuran daaka ]aukar mana mu masu karatunku kumamasoyanku.

Ina yi wa A’isha Ibrahim da Saratu Gi]a]o da BalarabaMohammed fatan Allah ya zaunar da su lafiya da mazajensu, amin.Ina gai da dukkan ’yan wasanmu na Hausa, maza da mata.Umar Shehu ‘Jana,’No. 41/42, Jibir Road, Minjibir, Jihar Kano.

YAYA ZAN IYA ZAMA DAN WASA?ZUWA GA MUJALLAR FIM,

DALILIN wannan wasi}ar shi ne in tambaye ku yadda zan yiin zama ]aya daga cikin ’yan wasa. Kuma ina son in zama

abokinku?Mekano,No. 1413 Kuka Daya, Nassarawa LGA, Kano.

Zai dace ka tuntu~i wani furodusa ko daraktan shirin fim ya gayamaka yadda za ka yi ka zama ]an wasa.

INA GAIDA MUSBAHU M. AHMADZUWA GA MUJALLAR FIM,

DALILIN wannan wasi}ar shi ne ina son ku mi}a min gaisuwataga mawa}in finfinan nan Musbahu M. Ahmad. Ina son ganin

Musbahu a finafinai saboda yadda nake }aunarsa. Kuma Allah yaja zamanin mujallar Fim da ma’aikatanta baki ]aya, amin.Bello M. Aliyu,NF 10B, Maiduguri Road, Kano.

KUKA GA ALI NUHU KAN KUDIRIZUWA GA ALI NUHU,

WANNAN wasi}ar na yi ta ne a kan wani fim ]inka mai suna{udiri. Na jima ina ganin finafinanka, amma ban ta~a ganin

fim ]in da bai yi ma’ana ba irin {udiri. Hujjata ita ce ni dai tun dana taso na san Musulunci,, ban ta~a sanin cewa Musulunci ya yardada wa ya auri matar }aninsa kamar yadda a fim ]in Zulkifilu yaauri matar }anin Ali Nuhu ba. Saboda haka don Allah ku gyarakuskurenku. Wassalam.Alh. Hadi Mohammed,Hausari Ward, Maiduguri, Jihar Borno.

SHAWARA KAN ‘AREWA AWARDS’ZUWA GA MUJALLAR FIM,INA fatan Allah ya sa mun shiga sabuwar shekarar 2002 lafiya. Inafatan dukkan ma’aikatan mujallar Fim za su ci gaba da ba dagudunmawarsu wajen ganin ci gaban wannan mujalla mai farinjini. Ha}i}a wannan mujallar ita ce jagorar mujallun Hausa!

Bayan haka, mun ga yadda aka yi bikin finafinan Arewa a cikinshekarar 2001, mun ga yadda ta kaya. To, ni a nawa ra’ayin ba waina ce abin da aka yi ba a kyauta ba ne, a’a, sai dai ina son ko me zaa yi to a duba cancanta, bajinta da }wazon da ]an wasa ya yi ashekara. Wannan zai }ara ]aukaka da kuma inganta harkar fimgaba ]ayanta.

Ra’ayina ya yi daidai da abin da wata Ummi [antsoho Mai FataBakin Kasuwa Wudil ta aiko maku (Fim ta Nuwamba 2001). Agaskiya ni a hangena idan za a bi irin wa]annan shawarwarin dawannan mata ta fa]i, to za a samu ci-gaba sosai a harkar fim.

Ina son in yi amfani da wannan damar domin in isar da sa}onta’aziyyata ga ilahirin ’yan fim da kuma iyalan marigayi daraktaU.S.A. Galadima da na marigayiya Fatima Mohammed Bature,wa]anda suka rasu a }arshen 2001. Allah ya ji}ansu da rahamakuma ya kyauta }arshenmu, amin.Aminu Ahmed Mohammed,Daki-Tara, Kofar Kaura, Katsina.

ABIDA INA TSAKANIN SON KIZUWA GA ABIDA MOHAMMED,

INA son in bayyana maki irin burge ni da kike yi a cikinfinafinanki. Har ta kai fim idan ba ki a ciki ba zan kalla ba kwata-

kwata, kuma idan ina kallo matu}ar kin fito to kuwa sai na yi karia jikin TV yara sun ]ebe. Da fatan kullum za ki ci gaba da ba nisha’awa. Kai, a ta}aice ban isa na misalta irin }aunarki da takezuciyata ba!

Kuma Abida, a cikin Mujadala kin ciri tuta, don kuwa wallahikin fi kowa cinyewa a fim ]in. A ta}aice, idan aka dubi fim ]in daidon basira, kin fi kowa cinyewa, musamman wani ]aurin]ankwalin da kika yi, ai wato shi ka]ai ya fi duk fim ]in! Kai daAllah ya sa kuna zuwa Azare, to da duk samarin wannan }auyenamu Gambaki sai mun cika Azare. To amma dai in Allah ya kawoki wata rana, to ki matsa ki zo Gambaki. Daga }arshe ina makialbishir idan har matata ta haihu kuma mace, to na yi maki al}awarinza ki samu takwara; a yanzu ma ko yau ko gobe haihuwar.Mashasha Mai Goro,Bakin Kasuwa, Gambaki, c/oYakubu Sulaiman Gambaki,Katagum LGA, Jihar Bauchi.

Page 12: Mujallar FIM - March 2002

Fim, Maris 2002 11

Sabon Titin Mandawari, Kano, Tel.: (064): 640341

ke gabatar da

}asaitaccen fim ne wanda aka da]e ba a yi kamarsa ba, kuma wanda ba za a yi “Allah-ya-isa” ko asarar ido ba.

Fim ne da ya }unshi talauci, arziki, sarauta, mu}ami, nisha]i, tsanani, rufin asiri, da sauransu

Zai fito nan ba da da]ewa ba. Ku neme shi, ku saye shi, domin sayen nagari maida ku]i gida.Duk wanda ya sayi Buri, to ya tabbata burinsa zai cika!

*Kada ku manta, shirin A’isha 2 ya fito, ku neme shi a kasuwa.

Wasu sababbin finafinan namu, wato Turba da Halak, su ma suna kan hanya.*

Iyan-Tama Multimedia su ne suka shirya maku }asaitattun finafinan da suka ha]a daBada}ala, {ilu Ta Ja Bau, Na San A Rina, Saudatu, Wa Ya San Gawar Fari?, A’isha, Fallasa,

Gashin {uma, Ha}uri, da kuma Dawayya

Iyan-Tama Multimedia... Da mai kama ake yin }ota!

Page 13: Mujallar FIM - March 2002

Fim, Maris 2002

Wasi}u ta hanyar ‘E-mail’Muna so masu aiko da wasi}a ta hanyar Intanet su ri}a sa cikakken sunansu da adireshinsu, ba adireshinsu na ‘e-mail’ kurum ba.

Muna da damar mu }i buga duk wasi}ar da ba mu yarda da ita ba ko don ba ta ]auke da cikakken suna da adireshi.

Adireshinmu shi ne:[email protected]

MAI ISKA, DAWO DA TALATUZUWA GA MUJALLAR FIM,

TARE da fatan dukkan ma’aikatanku suna lafiya. Bayan hakadon Allah muna ro}on Sani Mai Iska ya duba yiwuwar dawo

da matarsa Talatu, domin a gaskiya mu masoyan Fati Mohammedmuna son ta dawo.Tasi’u Musa,<[email protected]>

KU SADA NI DA MARYAM UMARZUWA GA MUJALLAR FIM,

BAYAN dubun gaisuwa da fatan alheri, ina mika sakon gaisuwata musamman zuwa wannan kamfanin mujallar Fim da

ma’aikatansa gaba ]aya.Ina so in sami wannan dama in ro}e ku ku ba ni adireshin i-mel

ko na gida ko ofis na Maryam Umar Aliyu, kuma ku aika min dasa}on gaisuwa ta musamman gare ta.Abba Tijjani,19-20, Lozumba Complex Area 10, Garki, Abuja.Tel: 09-2344610, 0802-3046806 <[email protected]

YABO GA MOMOZUWA GA AMINU SHARIFF,

A GASKIYA ka burge ni a fim ]inka na {auna kuma an yi mindaidai da aka ba ka award, musamman inda kake cewa ni ma

ai ina yi, ka fa]a ma Hadiza zan so na zo mu zama abokai sai dai niba a }asarku nake ba, ina karatu a Cambridge University, a Ingila.Amma don Allah ka aiko min da wasi}a, ni kuma na yi al}awarinidan na zo gida Nijeriya zan neme ka mu }ara sanin juna. To, saimun sadu. Tare da soyayya a yanzu da kuma koyaushe.Sakina Abdullahi,<[email protected]>

INA NEMAN SU IYAN-TAMAZUWA GA MUJALLAR FIM,

INA neman adireshin Hamisu Lami]o Iyan-Tama da IbrahimM. Mandawari da A’isha Ibrahim ko kuma duk wata hanya da

zan sadu da su. Ko dai hanyar adireshin i-mel, lambar waya koakwatin gidan waya. Na gode.Maryam(Gimbiyar Kano)USA [email protected]

Za ki iya tuntu~ar Iyan-Tama ta lambar tarho (64): 640341; shikuma Mandawari, lambar wayarsa ita ce: (64)-640310, sai adireshini-mel ]insa shi ne [email protected]; ita kuma A’isha, za kiiya buga mata waya ta wannan lambar: (62) 244244. Da fatan za adace.

BAN SAMUN MUJALLA A LEGASZUWA GA MUJALLAR FIM,

GAISUWA mai tarin yawa da fatan alheri. Ina fatan kuna lafiya.Ina kuma fatan ayyuka suna tafiya kamar yadda kuke bu}ata.

Allah Ya sa hakan, amin.Na yi muku marhaba da ganin wannan mujalla, koda shike kun

da]e da fitowa amma saboda ba mu samunta a nan Lagos shi ne yasa wasu sai dai su ga tallarta a cikin fim. Saboda haka, don Allah

ku aiko mani da fom da zan cika in biya ku]i ku ri}a aiko mani daita a koyaushe.

Bayan haka, shin kukan kar~i rubuce-rubuce daga jama’a kuwa?Zan yi murna in kuka rubuto mini amsa ta i-mel da wuri. Na gode,ku huta lafiya.Salisu Muhammad Dawanau,<[email protected]

Malam Salisu, ai ana sayar da wannan mujallar Fim a Legas.Bayan haka, idan ka aiko da sharhi mai ma’ana za mu buga.

BALARABA KIN MORI MIJIZUWA GA BALARABA MOHAMMED,

INa taya ku murnar yin wannan aure da Kumuri, da fatan Allahba da zaman lafiya.

A’isha Abdullahi<[email protected]

GAISUWA da fatan aalheri. Ku yi ha}uri na rubuto makuwasi}ar nan da Turanci ne domin ya fi yi min sau}i da sauri.

Ina so ku shawarci ’yan wasa su yi }o}ari su mallaki adireshin i-mel saboda mu masu }aunarsu mu samu damar yi masu wasi}u akan finafinansu.Abdulrahman Galla<[email protected]

NA JI DADIN GANINKU A INTANETZUWA GA MUJALLAR FIM,

Ina mai matukar murnar ganin mujallar fim a intanet. A gaskiyaabin ya ba ni mamaki da na duba kanoonline ]in kuma kawai saina ga wai an saka ta don mu samu mu kalla. Muna ta neman yaddaza mu ri}a samun sayenta wata-wata amma da yake gari ya yi nisaba mu samu.

To, ina dai so in gabatar maku da kaina kuma in shaida makucewa mutane suna yabawa da }o}arin da kuke yi a mujallar Fim.Ga adireshina nan na i-mel, kuna iya rubuto mani wasi}a akoyaushe. Haka kuma za ku ri}a ganin nawa wasi}un, domin nima ina matu}ar son finafinai. Kuma ga tambayata: na karanta labarinIbrahin Maishunku a Fim ta Disamba. Shin ko da akwai adireshini-mel ]in sa?Jamila Fagge<[email protected]

Hajiya Jamila,Mun gode da samun wannan wasi}ar taki. Muna fatan za ki ci

gaba da rubutowa. Ba mu da adireshin adireshin i-mel naMaishunku. Kuma gaskiya yawancin ’yan fim ]in mu ba su da i-mel. Amma za mu tambayar maki shi mu ji ko yana da shi. Mun

gode.

’YAN FIM KU SAMU I-MEL MANAZUWA GA MUJALLAR FIM,

12

Ku Zo Mu Yi Hira A Intanet!Masu sha’awar furta ra’ayi a kan harkar finafinanHausa a intanet za su iya shiga wani zaure mai suna“Finafinan Hausa,” wanda aka bu]e a }ar}ashin tsarin‘Groups’ na Yahoo, su fa]a. Za ka iya zama memba nazauren ta wannan adireshin da ke }asa:http://groups.yahoo.com/group/Finafinan_Hausa/join

Page 14: Mujallar FIM - March 2002

Fim, Maris 2002

’YAN WASA A DAINA WULAKANCIZUWA GA MUJALLAR FIM,

GA wata shawara ga dukkan ’yan wasan kwaikwayo. Don Allah akwai wasu daga cikin ’yan wasa da suka ]au duniya da

fa]i, wai a ganinsu ha]a]]u ne su (filmstars).Wani lokaci ma idanwani masoyinsu ya kai musu ziyara sai su dinga ji ji da kai, anawani hura hanci wai su ga ha]a]]un ’yan wasa. To, don Allahmasu irin wannan hali su daina, domin a ganina hakan ba shi dakyau.

Ya kamata mai irin wannan hali ya bari ya gama gogewa tukunna,fim ]in Hausa ya }ara daraja a idon duniya, kafin ya yi wanitun}aho. Dalilina na cewa haka shi ne akwai wani lokaci da waniabokina ya ha]u da wani ]an wasa a wani kanti ya je sayayya. Saiwannan aboki nawa ya je don su gaisa, amma ga mamakinsa sai]an wasan ya yi masa tarba ta wula}anci. Ina so fa duk wani ]anwasa ya gane cewa har yanzu wasan kwaikwayo yake yi, bai wucea ce masa ]an wasan kwaikwayo ba. Da fatan za su ]au wannanshawara tawa, amin.Rabee’u Bebeji<[email protected]>

AMINU KA FARA FITO DA ZAGE-ZAGIZUWA GA AMINU,

KA burge ni da fim ]in ka mai suna Asali. Yanzu na ga alamarZage-zagi sun taso.

Muhammed Bello Dikko,[email protected]

IN AIKO DA RAHOTO?ZUWA GA MUJALLAR FIM,

DANGANE da maganar da muka yi da kai na cewa, zan ri}aaiko da rahoto a kana bin day a shafi fina finai a nan Jihar

Zamfara, to, kasancewar an sami lokaci mai tsawo, ko zan iya inaiko da rahotonnin ta hanyar intanet, ko kuwa kun sami wani wandazai yi hakan?

2. Muna son a ba mu cikakkcen adireshin Hadiza Kabara.Abubakar Abdullahi Dangata,Government House, Gusau, Jihar [email protected]

Malam Abubakar, mun sa ido mu ga rahotanninka a kan }aidojinda muka tattaunawa da kai. Edita

TSOKACI A KAN WAKOKI A FIMZUWA GA MUJALLAR FIM,

MANZON Allah (s.a.w.) shi ne wanda wasu mutane suka ]aukada daraja, shi ya sa suke ~ata lokacinsu da }wa}walwarsu

domin wa}e shi da da]a]an kari.Wasu ’yan wasan Hausa sun gano cewa ba shi Annabin rahama

ya kamata a wa}e dakari mai da]i irin wannan ba; zai fi dacewa dasaurayi ya wa}e budurwarsa a cikin shirin fim ba ma a gaske ba.Allah ya shirya.Abubakar Aminu<[email protected]>

’YAR HANCIN BIBA A CIKIN YAQINIZUWA GA MUJALLAR FIM,

INA son ku ba ni dama domin in bayyana ra’ayina game da ’yarhancin da Biba ta saka a cikin shirin nan na Yaqini. Alal ha}i}a

wannan ya maida ta cus. Don Allah ta daina sa shi, in dai don adone take sa shi. Wassalam.Tasi’u Z. UsmanDept. of Accounting, University of Abuja.<[email protected]>

YA ZAN SAMU MUJALLA A MASAR?ZUWA GA MUJALLAR FIM,

NA rubuto muku wannan ’yar takardar ne domin in nunacikakken goyon baya a gare ku. Allah ya yi muku jagora. Sai

babban ba}in cikina shi ne rashin samun mujallar Fim a ko dayaushe. Don haka nake tambaya ko akwai hanyar da zan bi don narin}a samunta a kowane wata? Domin ba zaune nake a Nijeriyaba, yanzu ina zaune ne a Egypt (Masar) ina karatu a wata jami’a dake can. Don haka nake bu}atar ku ba ni shawara kan yanda zan yina rin}a samunta a nan inda nake.

A }arshe ina mi}a gaiwata ga A.A. Shariff (Momo), IbrahimMandawari, Hauwa Ali Dodo (Biba) da Wasila Isma’il.Abdulkadir WaziriBlock Bank Faisal G-7, Islamic Mission Hostel,Darrasa, Cairo, Egypt.abwazaid “ <[email protected]>

 Za ka iya karanta mujallar a ko’ina kake a duniya ta hanyar

intanet. Adireshin shi ne: www.kanoonline.com/publications.

KUN KARA MANI ILIMIZUWA GA MUJALLAR FIM,

MANUFAR ilimi ita ce ta sau}a}a tunanin ]an’adam, wannanwata a}ida ce tawa. Kuma babu inda na ga an sau}a}a tunani

kamar sharhin da Ibrahim Sheme ya yi a kan batun amfanin intanetga ’yan fim, wanda ya rubuta a cikin mujallar Fim ta watan Satumbada ya wuce. Kwanan nan ne na ga sharhin a lokacin da nake lilo aintanet ina neman rubuce-rubuce a kan batun hanyoyin sadarwa nazamani, inda na rubuta kalmar “Internet” ba daidai ba, na sa “TA”(wato intanet) maimakon “TER” (wato internet). To, kafin ka cekwabo sai aka wurgo mani mujallarku ta hanyar na’urar da ke nemowa mutum wani abu a intanet. A gaskiya wannan ya kasance ]ayadaga cikin lokuta mafi da]i a gare ni tun daga lokacin da na faraneman ilimin kimiyyar sadarwa.

A da, yawancin ]alibaina da ’yan’uwana sun kasa fahimtar abinda nake nufi da ‘E-mail’ da’ Internet.’ Amma sharhin Sheme yabayyana wa]annan abubuwa a cikin furuci mafi sau}i ta yaddakomai }auyancin mutum zai fahimce su. Kawai sai na ga ina tabuga sharhin daga printer ]ita kuma ina yin kwafe ]insa ina baduki wani Bahaushe da nake so in gaya wa yadda intanet take. Nagode }warai da }o}arin Ibrahim Sheme.I.A. [email protected]

13

SAUDAT FILM PRODUCTION, KANOKE GABATAR DA SHIRIN

Fim ne wanda yabambanta da sauran

Wadda ta shirya: HINDATU BASHIRWanda ya ba da umarni: SULAIMAN SA’EED’Yan Wasa: Hafsatu Sharada, Sulaiman Sa’eed,A’isha Bashir, Hindatu Bashir, Abdullahi Zakari,Dan’azumi Baba, Kabiru Maikaba, Shu’aibu Lawan,Alasan Kwalle, Hajara Usman...

Shirin MAULA zai fito a nan gabaka]an!

Page 15: Mujallar FIM - March 2002

Fim, Maris 2002

Ku

sufilin: “Filin Ku Tambaye Su, Fim, P.O. Box10784 Kano”.

Don haka ga fili nan ga doki!

]aukar hoto, dillalan kaset da sauransu... A wannansabon filin mai suna “Ku Tambaye Su,” za ku iya yimasu duk tambayar da kuke so, kuma za su ba kuamsa. Sai dai muna fatan duk tambayar da mutum zaiyi, ya tabbatar tana da ma’ana, kuma ya sanyacikakken sunansa da adireshinsa. Kuma tambayar takasance ta}aitatta, babu dogon Turanci.

A jikin ambulan ]in a tabbatar an rubuta sunan

Masu karatu, kuna da tambayar da kuke son ku yi wa ’yanfim kai tsaye su ba ku amsa? Wato ’yan wasa, daraktoci,furodusoshi, mawa}a da maka]a, marubuta labaran fim, masu

14

NORTHERN STAR FILMSPRESENTS

Produced by FIM MAGAZINEDirected by HAFIZU BELLO

Stars: Sadiya Abdu Rano, Musbahu M. Ahmad, Sani Moda, Aliyu Gora, HindatuBashir, Isa Ja, A’isha Ibrahim, Mika’il Hassan ‘Gidigo,’ Baban Mulika, Shu’aibu

‘Kumurci’, Ashiru Bazanga, Saratu Gidado, Shehu Kano, Galin Money, etc.Story/Screenplay: Iro Mamman; Camera: Yahaya Skito

WAIWAYE

Akwai ’yan mata da damawa]anda yanzu sun riga sunshiga kuma tuni suna cikisuna ta ]aukar darussa. A’ishaIbrahim ita ma ta samu cinjarabawa zuwa ‘A.B.U.’, saidai tana gida tana jiran a kawomata takardar shaidar ]auka(admission letter).

Rabi Mustapha kuwa makouku da suka gabata ta shigatata makarantar. Yanzu tanacan a matsayin JJC, sai nangaba za ta zama ’yar gari.

A Kaduna, Asabe Moham-med, zabiyar nan wadda ta yiwa}ar cikin Dare [aya, ta yi

aurenta, sannan a Gusau kumaAliyu Abdullahi, jaruminshirin Ki Yafe Ni, ya samuyafewa daga gun kyakkyawarbudurwarsa Asiya har sunshiga jami’ar taa aure.

Fitaccen ]an wasa Shu’aibuLawan (Kumurci) da BalarabaMohammed su ma sun zaunajarabawa lokaci ]aya, iri ]aya,kuma sun ci; tuni sunayensuna cikin jami’a za su fara]aukar darasi iri ]aya a cikinaji ]aya kwanan nan.

Ba su ka]ai ba, kada kumanta [an’azumi Baba daTijjani Asase kwanan bayasun fara yin digirinsu na biyua cikin ‘A.B.U.’ To, kwanannan kuma wasu ’yan fim sun]auri aniyar shiga wannan}asaitacciyar jami’a da zararwannan watan na Maris yakama.

Furodusan Tsaro, Musa

Liman Jalingo, shi ma a ran 8ga Maris zai je Jalingo yakar~o takardar shaidar]aukarsa a jami’ar.[an’uwansa ]an wasan nanDailami, shi ma tuni ya samushiga har ya fara ]aukardarasi.

Jami’ar ‘A.B.U.’ ta fara cikada ’yan fim!

Wace wainar sukatoya a Makka?WANI abin alfahari da

ke faruwa a cikin’yan fim yanzu shi

ne yawan aure-auren da sukeyi, ko dai tsakaninsu ko kumasu fita wajen duniyar fim suauro. Wannan yana }ara}aryata zargin da wasu ke yicewa ba su yin aure.

Daga 2001 zuwa yau za aga cewa ]imbin ’yan fim sunshiga ‘A.B.U.’, wato jami’arda aka fi sani da suna ‘AureBautar Ubangiji.’

Abin sha’awa kuma shi neyadda fitattun ’yan mata kesamun shiga jami’ar kai tsaye.

HAUSAWA na cewashekara kwana. Idan ba kumanta ba, shekararda ta gabatamun ba ku labarin wainar daIbro da Mandawari suka toyaa }asar Saudiyya a lokacin dasuka je yin aikin hajji.

A bana a wata na gaba, zamu ba ku cikakkun bayanan

wainar da wasu ’yan fim sukatoya a hajjin wannan shekarar.

Duk da ]an karen tsadar daku]in kujera ya yi, ’yan fimda dama sun sauke farali abana. Daga cikinsu akwaiIbrahim Mu’azzam nakamfanin Zinariya; YakubuMuhammad da amininsa SaniMusa Danja na ‘Two EffectsEmpire’; Kabiru Mohammedmai ‘Zainab Film Production;’Baba Shariff wanda shi nesakataren {ungiyarFurodusoshi ta Jihar Kano, dakuma wasu da dama.

Sani Musa Danja

Page 16: Mujallar FIM - March 2002

Fim, Maris 2002

ABOKANMU

Jamil B. Nasir KalahUnion of ProfessionalPhotogaphers, Gusau,Jihar Zamfara

Mariya ’Yar Shule MalamMalam Mai Zanen Hula,Gwalalo, PO Box 9,Gamawa, Jihar Buchi

Yusuf Nadabo Moh’d,Gold Face Foto, No. 6,Garkawa Street, Shendam,Jihar Filato

Alh. Aliyu (ManagingDirector), A.A. InvestmentsLtd., P.O. Box 2571,Sokoto

Wasu masu karatu suna aiko da hotuna marasa kyau: ko sun yi duhu,ko wanda ke ciki ya yi nisa. Ba za a iya amfani da irin wa]annan ba!A tabbatar hoto ya fito ra]au, kuma a sa cikakken adireshi.

Furodusoshi da daraktoci da ’yan kasuwa masu dabara dahangen nesa ne suke saka tallarsu a cikin mujallar Fim

Abdullahi Isma’ila (RN, rnt,rgc, dhn, cmd, nmce), Sch.of Nursing, Birnin Kudu,Jihar Jigawa

Shafi’u B. Mohammed,Oasis Air Servies Ltd., No.61 Ibrahim Taiwo Rd., POBox 437 Kano. Tel: 641050

Mustapha Challuba,Insha Allahu Oil Nig.Limited, P.O. Box 1661,Gamboli Rd., Maiduguri

Moh’d Farid Dauda,No. 18, Alhaji Maje Road,Tudun Wada, Zariya, JiharKaduna

15

Zainab da Salim A.A. Rasheed, No. 6/8 New Central Park(babbar tashar motar Kawo), Kawo, KadunaTel.: 062-316059

Yusuf Suleiman MusaGyadi-Gyadi,Dept. of Accountancy,University of Maiduguri

Suwaida AbdurrahamanUba Ringim, Fagge D.,Kano; Tel.: 064-634329

Page 17: Mujallar FIM - March 2002

Fim, Maris 2002

ABDULLAHI Zakari wanda aka ji sani dasunan Ligidi, sunan da ya samu a shirinWasiyya, yana daga cikin wa]anda mugunha]arin nan da wasu ’yan fim ya rutsa da sua hanyar Kano zuwa Katsina a bara. Idan kuntuna, a labarin da muka ba ku a Fim ta watan

Yuli 2001, mun gaya maku cewa a ha]arin ne darakataAminu Hassan Yakasai da ’yar wasa Maijidda Mustapha sukarasu. Ligidi yana daga cikin masu kwana gaba, sai dai ya

sami munanan raunuka a jikinsa. Raunin da ya samu ne yakai shi ga yin kwanaki a kwance a asibitin ‘KhadizaMemorial Hospital’ da ke Kano. Ligidi ya shaida wa Fimkwanan nan cewa dukkan kwanakin da ya yi a asibitin bai

san inda yake ba.Su mutane, ganin cewa Ligidi ya fita daga

hayyacinsa, sai suka yi zaton ko hankalinsa ma yafita daga }wa}walwarsa. Aka ri}a kallonsa amatsayin kwarkwar. Wannan ne ya sa aka ri}a ~oyemasa labarin mutuwar Aminu da Maijidda. Lokacinda Abdullahi ya baro asibiti, duk inda ya tunkarigungun ’yan fim sai ka ji ana cewa a cikin ra]a,“Ga Ligidi nan kada ku gaya masa komai; har yanzukansa ba daidai yake ba.”

Mu kanmu a mujallar Fim, an gaya mana haka,saboda haka wata rana da Ligidi ya ziyarci ofishin,sai muka kasa yi masa maganar ha]arin.

Shi kuma gogan naku duk inda ya je sai ka jiyana cewa, “Wai ina Aminu Hassan?” Aminu daiabokinsa ne tun suna yara matasa. Iko sai Allah!Mutane sai su amsa masa da cewa, “Aminu ya tafiAbuja, ita kuma Maijidda ta tafi garinsu Funtuwa.”Wannan ne kuma ya ri}a fusata Ligidi, duk inda yaje sai ya ri}a ya]a maganganu kan marigayi Aminu,yana cewa, “Yanzu shi Aminu yana ganin halin danake ciki amma sai ya tafi ya bar ni?” Abin dariya,abin tausayi, da Ligidi ya bar wajen sai a ri}azun]ensa, ana cewa, “Ya fa ta~u! In ba ta~a~~e bawa ke tambayar matattu?”

To }arshen tika-tika dai an ce tik! Ligidi ya warkesarai. Yanzu ko o’o bai fi shi hankali ba. ’Yan fimkuma sun rungume shi, yana ta harkarsa kamaryadda ya saba yi kafin ha]arinsu. Sai dai ya fusatada yadda aka ri}a yi masa mummunar fahimta dakuma yadda aka ri}a ~oye masa mutuwar Aminu.Ya yi tattaki ya zo ofishin mujallar Fim na Kano aranar 21 ga Janairu, 2002 don ya tabbatar wa jama’acewa bai ta~u ba, kansa garau yake har yanzu, yananan a Ligidinsa. A cewarsa, shi dai bai ta~u ba, saidai kawai jama’a ne suka haukata shi.

Ga yadda hirar ta kasance:Fim: Ligidi, me za ka iya cewa dangane da

ha]arin da kuka yi a tsakiyar shekara ta 2001 kan

Ha]arin ’yan wasa a hanyar Katsina

MUTANE NE SUKA

– inji Ligidi

Malam Abdullahi Zakari (Ligidi)

16

Page 18: Mujallar FIM - March 2002

Fim, Maris 2002

Alhaji Abdulrasheed

Shaguna Masu Lamba 6 da 7, da 8, Babbar Tashar Mota ta Kawo, Kaduna, Tel.: 062-314033

A shagon ALHAJI ABDULRASHEED ne ka]ai za ku samiingantattun finafinan Hausa na da da kuma na yanzu wa]anda kefitowa a kowane mako.

Za a kuma samu finafinan Indiya tsofaffi da sababbi; ga Chanis,da kuma finafinan Makosa; ga na addini Hausa da Turanci, gakuma finafinan bidiyo CD iri-iri sai an darje.

Akwai kuma kaset-kaset na rediyo na Hausa da ke fitowa akowane mako, da dai rediyo kaset iri daban daban.Kayayyakinmu suna da sau}in farashi ga masu sari ko sayen ]ai]ai.

Ziyarce mu a shagunanmu da ke Babbar Tashar Motar Kawo

GANI YA KORI JI!!

hanyar Katsina?Ligidi: Gaskiya wallahi ba zan iya cewa komai ba; na san

dai kawai za mu tafi Katsina, muna tafiya muna hira munadariya. Amma daga }arshe ban san abin da ake ciki ba saidaga baya bayan ma na fito daga asibiti ake gaya min. Dafarko ma ban san wa]annan ’yan’uwa nawa (Aminu daMaijidda) sun mutu ba.

Fim: Ka san lokacin da aka kai ka asibiti?Ligidi: Wallahi ban sani ba.Fim: Kwana nawa ka yi sa’annan ka san kana asibiti?Ligidi: Sanina kawai ranar da na farka na farfa]o sai na

gane cewa a ina nake? Sai dokta ya ce min a sibiti nake. Saina ce a sallame ni na warke.

Fim: Kwana nawa da kwantar da kai a ranar da ka yiwannan magana?

Ligidi: Kwana goma sha ]aya.Fim: Lokacin da aka sallamo ka mutane sun yi ta cewa

kamar }wa}walwarka ta ]an ta~u.Ligidi: Gaskiya ni dai an ~oye min mutuwar marigayi

Aminu Hassan da aka ce min, “Ai ya samu sau}i ya ma tafiAbija; wannan yarinya kuwa (Maijidda) tana Funtuwa,}afarta ce ta ]an karye ka]an.” Saboda haka sai na ri}a yawoina cewa, “Maimakon su tsaya su gan mu sai su tafi unguwa?”Mutane sai suka ri}a ]auka kamar maganganun da nake, kona ]an samu matsala ne a }wa}walwata, wai na ]an ta~u.Sai bayan da na gane cewa sun mutu sa’aman mutane sukagane ashe rashin sanin da na yi ne, amma ba haka nake ba.

Fim: Yanzu me za ka ce wa mutanen domin su ne suka~oye maka labarin mutuwar?

Ligidi: Gaskiya su ne suka hauka ta ni. Amma ni inatabbatar masu da cewa lafiyata }alau, babu abin da ya sameni. Kuma abin da na saba yi duk ina yi, ina zuwa shirya fim.

Fim: Lokacin da aka yi ha]arin, wasu sun ce }afarka takarye, wasu kuma sun ce ai kanka ne ya bugu. To me yasame ka?

furodusa/darakta.

SATARAMSA:Bai yiaure batukuna,kuma yat a ~ az a m azakara ag a s a rs h i r i nfim.sa’annana Kanoyake!Waneneshi? Saia rubutoda sauria gayamana. Wanene wannan yaron?

GASA TA 13Wanene wannan?Wannan ]an yaron da kuke gani, ba yaro ba ne a yau.Matashi ne, jarumin finafinai ne da dama a yau, kuma

17

Page 19: Mujallar FIM - March 2002

Fim, Maris 2002

Ligidi: Karaya ce a kafa]ata kumata ]an shiga ciki. Nan hannuna (ya nunahannunsa) ya yanke, jini ya zuba sosai.Na kuma samu targa]e, har yanzu yanayi min ciwo; ban da kuma ’yanciwurwuka da na ]an samu.

Fim: To duk inda ka je idan an cemaka sun yi tafiya ba ka ji kamar suntafi sun yada ka ba?

Ligidi: Ni dai fa]an da nake kawaishi ne kamata ya yi su tsaya don jama’asusan muna nan ba mu mutu ba. Ashe~oye min aka yi, ni kuma na yi tacigiyarsu bayan babu ransu!

Fim: To ka ba masu karatu cikakkentarihinka yadda za su }ara tabbatarwakana nan garau.

Ligidi: An haife ni a 1963. Na fara‘Jar}asa Primary School’ a nan Kano,daga nan na tafi ‘Kumbotso TeachersCollege’. Na gama a 1985. A 1986kuma na tafi a ‘Bayero na yi digiri ]inana farko a fannin siyasa (PoliticalScience). Har yanzu ina aiki dama’aikatar ilimi; ina koyarwa ne amakarantar ’yan mata ta Giginyu.

Fim: A wace shekara ka fara harkarfim?

Ligidi: Na fara harkar fim a 1984 harzuwa yanzu.

Fim: A wancan lokacin da me ka farakuma su waye abokan shirinka?

Ligidi: Lokacin na fara tun inamakarantar sakandare, muka kafa

}ungiya ta Gyaranya wadda yanzu takoma ‘Tauraruwa’. Lokacin muna tareda su Alhaji Gyaranya, da su Bashir I.Bashir da su Iliya.

Fim: Lokacin kakan yi wasa natalbijin?

Ligidi:Muna yin wasa a NTA daCTV, daga baya kuma sai muka komana bidiyo.

Fim: Daga wace shekara aka faranuno ka a talbijin kana wasa?

Ligidi: Daga 1987.Fim: Wane wasa ka fara yi a lokacin?Ligidi: Akwai wani wasa da ake kira

Farin Wata. Muka kuma yi ZakaranKekuwa a NTA da Cinnaka. Lokacinakwai su Banono, Shehu Hassan, dawani mai suna Abdullahi MusaKwazari da Mohammed Lawan wanda

ya rasu.Fim: Daga yaushe ka fara wasa na

bidiyo?Ligidi: Na fara na bidiyo a 1990. Sai

dai mun fara tun kafin lokacin, ammabai fita ba sai 1989 zuwa 1990.

Fim: Da wane fim ka fara?Ligidi: Wani fim ne da ake ce wa Ko

Da Me Ka Zo, akwai Karen Bana, dawasu.

Fim: To na baya-bayan nan fa?Ligidi: Na yi finafinai da yawa

wa]anda ba zan iya lissafa su ba.Amma fim ]in da aka fi sanina da shishi ne Wasiyya, tunda a cikinsa ne nasamu sunan Ligidi. Kuma ina da wasumasu ]imbin yawa.

Fim: A cikin fim ]in Badali ka fito amatsayin ]an sanda har wasu na cewashin Ligidi bai ta~a yin aikin jami’intsaro ba?

Ligidi: Wallahi ban ta~a yi ba sai daina yi aiki ne da irin abubuwan da akace min in yi.

Fim: Wane matsayi ya fi burge kadaga cikin wa]anda kake yi?

Ligidi: Kowane, amma dai na fi sonna jami’in tsaro don in nuna abu marakyau da kuma mai kyau. Ban da Badalikuma a Hukuma da Rama Cuta dukna fito a matsayin jami’in tsaro, kumaakwai irinsu da yawa.

Fim: To Allah ya tsare mu.Ligidi: Amin. Na gode.

18

No. 21, Zaria Road, Gyadi-Gyadi, Kano, kusada Fly-over, gefen ofishin mujallar FIM

Tel.: 064-665482, 666419

Alh. Adamu A. UmarJanar Manaja

In dai ]inki mutum yake so nagargajiya ko na zamani, to ya zoshagonADAMU TAILORING/FASHION SERVICES

domin mun }ware a kan kowaneirin ]inki na maza ko na mata,yara da manya

{wararrun telolinmu sun da]e anadamawa da su a sana’ar ]inki, donhaka mutane da dama sukan kawoaikin ]inkinsu wurinmu.Me zai hana kai ma ka jaraba?Aikinmu akwai rahusa da biyanbu}ata.

[inki na gani na fa]a, sai

ADAMU TAILORING &FASHION SERVICES

Sai kun zo.

Gaskiya ni dai an ~oye minmutuwar marigayi Aminu Hassanda aka ce min, “Ai ya samu sau}iya ma tafi Abija; wannan yarinya

kuwa (Maijidda) tana Funtuwa,}afarta ce ta ]an karye ka]an.”

Saboda haka sai na ri}a yawo inacewa, “Maimakon su tsaya su gan

mu sai su tafi unguwa?” Mutanesai suka ri}a ]auka kamar

maganganun da nake, ko na ]ansamu matsala ne a }wa}walwata,

wai na ]an ta~u.

Page 20: Mujallar FIM - March 2002

Fim, Maris 2002

A u r e n

BALARABAda

K U M U R C I

MUJALLAR Fim ta saba tsinkayar ’yanwasan da za su yi tasiri a can gaba aharkar fim. Wannan ya sa tun BalarabaMohammed ba ta da]e da shigowa harkarfim ba sai mujallar ta yi hira da ita, akabuga a fitowarta ta watan Mayu 2001

inda aka yi mata taken cewa “Ta Fara Rage Tashen Wasu.”A cikin hirar, Balaraba, wadda za ta yi a cikin wannan watan,ta furta cewa ita da ma ba ta zo harkar fim ba ne don yinzaman dirshan a ciki. Cewa ta yi sha’awa ta kawo ta kumaba da da]ewa ba za ta yi aure. Ita dai tunaninta idan ta ta~awasu sai ta koma gida ta yi aure. Ashe abin ba haka yake ba.Barowar da ta yi wa Kaduna garin haihuwarta ta taho Kanoashe kira ne }addara ta yi mata. Allah Ya }addara a cikinharkar fim za ta samu mijin aure. Kuma ba wani furodusako darakta ba ne sai fitaccen ]an wasa Shu’aibu Lawan(Kumurci).

A duk ’yan wasan fim Kumurci ne wanda za mu iya cewashi ne na kusa wajen ma}wabtaka da ofishin mujallar Fimda ke Kano. Gidansu bai kai tazarar rabin kilomita ba. Bashi da wuyar gani a gida ko a cikin gari wurin fim. Tun

lokacin da soyayyarsu da Balaraba ta yi }arfi har maganaraure ta shiga ciki, kusan duk inda za su to tare za ka gansu. Wannan ya sa jama’a da yawa na ganin in dai zamanaurensu ya ]ore a haka, to ba }aramin dan}o zai yi ba.Wani abin sha’awa kuma shi ne, tun ba a yi auren baBalaraba ta zama tamkar ’yar gidansu Kumurci, kullumsai ta je gidan, wani lokaci ma har zama takan yi a yiwasu aikace-aikace da ita. Sai fa ranar da take da fim. Shikansa Shu’aibu ya samu kar~uwa matu}a ga mahaifanBalaraba a Kaduna. Domin ko zuwan da wakilin Fim yayi wurin mahaifin Balaraba sai da ya aika wa Shu’aibu dawasi}ar cewa ’yan mujallar Fim sun zo wurina, ina fatanba za ka damu ba.”

To Kumurci dai bai damu ba, don kuwa ya kai editaASHAFA MURNAI BARKIYA har cikin gidansu a ranar12 ga Fabrairu inda ya ga ana ta aikin gini ba }a}}autawa.Bayan nan kuma sai suka zauna a cikin ]akinsa ya fara bashi labarin yadda suka ha]u da amaryarsa, halin da akeciki, da kuma yadda yake ganin zamansu zai kasance.Shu’aibu Lawan dai shi Allah Ya bai wa Balaraba ammaba shi ka]ai ne ya neme ta da aure ba. Su wanene ya kasa?

Sarkin Mugunta a fim ya biya sadakin budurwar da Ibrahim Mandawari ya ta~a cewata fi kowace yarinya kyau a fagen fim. Nan da kwana ka]an za a yi bikinsu

Daga ASHAFA MURNAI BARKIYAda ALIYU ABDULLAHI GORA II

19

Page 21: Mujallar FIM - March 2002

Fim, Maris 2002

komai zan yi ba sai daigodiya. Ka ga na je ]aurinauren Fati amma jama’ata basu ma bari na }arasa can cikisosai ba saboda an yi minyawa. Shi kuma wannan]aurin aure namu abu newanda yake gaibi tunda bazan iya tabbatarwa za a je dayawa ba ko a’a. Na san daimutane da yawa sun shaalwashi. Wa]anda ke daniyya Allah Ya ba su ikonzuwa wannan ]aurin aure.

Fim: To ka dai ga yaddawasu suka yi aure ammaAllah bai sa ya ]ore ba. Kaiwane mataki ka ]auka na yiwa gulma kariya daga isa

Ko kuwa gammo ya yi yafasa kai zai kai masu sari saisuka firgita suka gudu?

Duk za ku ji a cikinwannan hira da aka yi da shilokacin kansa ya ]au caji: ga

dai aure ya gabato, ga kumaaiki a gabansa. Editanmu yafahimci kan nasa ya yi zafilokacin da ya yi masa tayinabinci. “Bismilla,” injiShu’aibu, amma tun kafin a

ce masa, “Alhamdu lillahi,”tuni har ya bu]e kwano.Ashe kwanon ba komai aciki. Haka Kumurci ya ri}emurfin kwanon abinci daBalaraba ta dafo ta kawo

masa yana dariya yana cewa,“To wallahi Sinana ne da yashigo ya cinye shi.” Sai daikuma ya ~ata fuska lokacinda aka katse masa dariyar dayake yi da tambayar farko:

Ban ta~a soyayya mai zurfi dakowa ba sai Balaraba, inji Kumurci

Fim: Kumurci, yanzu daika yi gammo ka fasa kai zaka sari Balaraba ko?

Shu’aibu: Ban gane ba! Nikuwa wane tsautsayi zai sain sari Balaraba? Sai dai insari mai }arar kwana. AmmaBalaraba? Ai inaaaa!! Ba daiita ba.

Fim: Nufina batunaurenku. Yau sauran kwananawa? Kuma ya aka yi kukaha]u?

Shu’aibu: Ni fa ‘Kumurci’ba sunana ba ne, suna ne nala}abi da na samo a cikin fim]in U}uba. Kuma ni bamugu ba ne, halayena bahaka suke ba. Don sabodakyawon halayena – duk dadai an ce yabon kai jahilci –Allah Ya ha]a ni da Balarabatun farkon zuwanta Kano.Soyayya ta shiga tsakaninada ita sosai, sai dai tun alokacin ba mu yi saurin furtazancen aure ba, sai dai kawaini na tabbata tsakanina daAllah da aure nake son ta. ToAllah kuwa ya }addara gashi auren ya zo ranar 15 gaMaris, 2002.

Fim: Lokacin da kuka faramaganar aure akwai wandaya nuna wa ]ayanku za asamu matsala ta~angarensa?

Shu’aibu: Dukkanmukowa ya fa]a, ita tana cewatana ganin daga iyayena zaa samu matsala ni kuma inacewa daga iyayenta ne za asamu matsala. Allah daikonsa dai ga shi ba a samuba sai dai ka]an daga’yan’uwa wani ya ce kazakaza, amma wannan baihana ni da ita mu }araamince wa juna ba.

Fim: Ko ka yarda cewa baa ta~a yin soyayya tsakanin’yan fim ba kamar kai da

Balaraba?Shu’aibu: Wannan duk

gaba ]aya yin Allah ne.Kuma ni kaina da na samukaina a wannan halin ban yimamaki ba saboda na sanbabu yadda Allah ba ya yi.Mun kasance da ni da ita bamu iya zama daban-daban,ko da yaushe muna tare.Kuma wannan aure zai }aratabbatar wa mutane cewa nimutumin kirki ne, ba yaddanake a fim nake ba.

Fim: Bisa dukkan alamu,za a yi taron jama’a sosai awurin ]aurin aurenka. Kokai ma ka fahimci haka?

Shu’aibu: E, to ai ba

Shu’aibu Lawan a matsayin Makau, mataimakin bos acikin Gagarabadau, shirin mujallar Fim

wurin amaryarka?Shu’aibu: Da ma ni

matakin da ni da ita muka]auka – saboda mun jiabubuwan da aka ri}a yi nazuga ga wata wadda ta yiaure daga mutane miyagu –sai muka ]auki mataki. A da,gida ne na haya na kama, harna biya ku]in sai babana yaba ni shawara cewa baikamata ba domin idan na fitaka ga saura ita ka]ai a gidan.Shi ne ya ce min in yi gini agidanmu. Sai na yi hakan.Ka ga ga shi nan an kusakammalawa. Kuma zaikasance }ofarta tana rufe bakowane ba}o ne za a ri}abari ya shigo ciki ba.

Fim: Me za ka ce wamasoya fim ]in Balarabadomin za ka ]auke masu ita?

Shu’aibu: Ai wa]annansai dai godiya, ai da ma sunsan ba sun dinga kallontahaihata-haihata ba. Kumaduk wanda ko wadda kekallon fim ]in Balaraba zaiyi farin ciki ya ga cewa ta yiaure domin ya sanconfirmed (ya tabbatar) tatsaida yin fim kenan.

Fim: Idan ka yi aure za kadaina kashe-kashe a fimkenan tunda za ka koma amatsayin maigida ba tazuruba?

Shu’aibu: Ai sai dai in}ara saboda ni don mutanesu }ara tabbatarwa ni mugune a fim mutumin kirki awaje.

Fim: Wane gari ka ta~azuwa ka samu ]imbinmasoya?

Shu’aibu: Ai ni tunda nafara fita na fara barin garinnan ba garin da na ta~a zuwaaka nuna kamar ba a san niba. Za mu tafi da yawa mazada mata amma sai ka ga na

20

Page 22: Mujallar FIM - March 2002

Fim, Maris 2002

yi fice, kowa sai ya ce niyake so ya gani, kuma niyake so ya ta~a. Wannanyana sa ni jin da]i }warai.Ina kuma }ara gode Allah akan wannan harka. Allahkuma ya }ara kare mu!

Fim: An ce wai ka ta~azuwa Ha]eja ka fito filinGala kana kirari sai wani yaba ka kyautar wu}a. Totsammani yake kai ko ]antauri ne?

Shu’aibu: E, akwai wandaya ba ni wannan wu}akyauta saboda shi yanaganin kamar ni ma ]antaurin ne. Kai ba ma shika]ai ba, akwai wanda ya}ero wu}a ya rubuta matasunan Kumurci. Tana nanyanzu haka da ita nake ’yanyanke-yanke a gida. Har nangida aka kawo min ita.

Fim: Ganin mutane natunanin ko kai mugu ne, toko wani ~arawo ko ]an dabaya ta~a latsa ka ya ga iyajaruntarka?

Shu’aibu: Babu wanimutum da ya ta~a tare da niya ce zai yi min wani abu.Kuma ni abin da nake yiyana ba ni kwarjini dominana yaba mani.

Fim: Kafin Balaraba ko kata~a yin soyayya da wata?

Shu’aibu: Gaskiya ni banta~a yin soyayya ba kafinBalaraba.

Fim: Wata}ila ’yan matankallon mugu suke yi maka.

Shu’aibu: A’a ba haka bane, ni da ma da na taso bantaso da yaudara ba. Abin dana ]auka idan mutun yanasoyayya ya bari, to yaudarane. Sai dai ’yar wadda ba arasa ba a unguwa. Amma niban ta~a yin soyayya dawata ba har ta tsaya min saiBalaraba har shi ne na ga yadace in aure ta.

Fim: Da an ]aura aure zaa tare ko sai an ]auki wanilokaci?

Shu’aibu: Ai mu Allah daikonsa so muke idan an]aura aure gaba ]aya za atare ba tare da an ]au wanilokaci ba.

Fim: Akwai wani shiri nabiki da kuka yi?

Shu’aibu: Gaskiya ba zaniya fa]a ba saboda abu newanda ya danganci ku]i. Zata iya yiwuwa abin da naketunani ya zama ban samu ba.

Ka ga na zama ma}aryacikenan. Amma dai kowa yasan duk inda za a yi bikikamar wannan dole za a yiwasu shagulgula wanda za atara jama’a a burge su.

Fim: Me za ka ce wasamari abokanka wa]andaba su da niyyar aure?

Shu’aibu: Kawai su sahimmar nema saboda ba zaniya kushe su ba sabodawannan abu Allah ke yinsa.Su ma akwai lokacinsu yanatafe.

Fim: Ga shi dai tun kafina yi aure kun sha}u da juna.Ko mutanen gidanku sunsan ta kuwa?

Shu’aibu: GaskiyaBalaraba a gidanmu babuwanda bai san ta ba tundakusan kullum ma in dai maba aiki gare ta ba tana zuwawurin matan yayyaina, za kaga suna yin yawancin komaitare. Kai in ba}o ne ma idanba ka sani ba sai ka zaci agidanmu take.

Fim: Me za ka ce wadaraktoci da furodusoshidomin ta dalilin fim ne harka ha]u da Balaraba?

Shu’aibu: Allah zan fara

gode wa wanda in ma]aukaka ne to shi ya ba ni.Su ma kuma na gode masusaboda hanyoyin da suka~ullo mana da su na samunabubuwan yau da gobe.

Fim: Ko akwai wasu ’yanfim ginshi}ai da suka tsayatsayin daka don ganinwannan aure naka yatabbata?

Shu’aibu: E, to, gaskiyaidan ma akwai to ni dai bansani ba. Ni mutum ne arayuwa ma na sani sabodaAnnabi (SAW) ya fa]a dukmutumin da ke son abunhannun mutane to mutane zasu guje shi, kuma idan kanuna ba ka son abun hannunmutane to sai su so ka.Gaskiya ni na bi wannan layidon haka ba na so in ga nayi relying (dogaro) da kowa.Wane idan ya yi min na sanlokaci ne yake da shi, wanekuma idan bai yi min ba nasan lokaci ne ba shi da shi.

Fim: Wa]anne finafinaine ka yi tare da Balaraba?

Shu’aibu: Akwai finafinaida muka yi da ita, wasu nasan su wasu kuma ban sansu ba, wasu kuma ba su fito

ba. Akwai Maryam 2, akwaikuma wani fim da muka yia Jos wanda a ciki ta fito amatsayin matata. Akwai fim]ina Gumbar Dutse da kumawani fim a Jalingo.

Fim: A }arshe mun san dawuya a ce yarinya kamarBalaraba kai ka]ai ne kaneme ta da aure; idan ba kaika]ai ba ne su wa ka kasa?

Shu’aibu: Gaskiya ba nika]ai ]in ba ne; akwaiwa]anda suka nuna sonaurenta amma dai sai tafahimci ni ka]ai ne dagacikinsu ke ba na sa mata}arya cikin lamurrana.Kuma wasu ma sai suka ri}akomawa bayan fage sunaneman ~ata abin har rashinjituwa ya ]an fara shigatsakani. Amma daga baya saita fahimci ’yan zuga ne, balaifina b a.

Fim: Sai kuka daidaita.Shu’aibu: Ta daidaitawa ai

ta }are har ga shi ma za a yiaure!

Fim: Allah Ya sa damu zaa sha biki.

Shu’aibu: Amin. Madalla,na gode.

Ko a rami Shu’aibu zai sakani na amince don ina sonsa

– inji Balaraba

Fim:Balaraba, kin ta~a bamu tarihin rayuwarki. Munaso ki }ara saboda wannanbiki naki da ke tafe.

Balaraba: Ni dai, niasalina ni Bafillatana ce,kuma a garin Kaduna akahaife ni. Mamana kumaainihinta ita BafillatanarChadi ce. A nan na yi

A wurin ]aukarfim ]in Tasiri 2 aKaduna kwanannan, Balaraba tagaya wa wakilinmura’ayinta a kanwannan auren nata

makaranta, kuma a nan garinKaduna na girma, har na zona fara harkar fim.

Fim:Shekarunki nawa dahaihuwa?

Balaraba: Ni yanzushekaruna goma sha tara. Toamma, ni na manta …..(dariya). To, amma kila nashiga ta ashirin!

Fim:Ke ce ta nawa gamahaifanku?

Balaraba: Ni ce ta hu]u.Fim: Za ki iya tuna

shekarar da kika fara shigaharkar fim?

Balaraba: Gaskiya ashekarar 2000 na shiga.

Fim:Da wane fim?

21

Page 23: Mujallar FIM - March 2002

Fim, Maris 2002

ina son shi. Shikenan mukayi magana, muka ga yacancanta mu yi auretsakanina da shi.

Fim:Ke kika faratuntu~arsa da maganar aureko shi ya fara?

Balaraba: Gaskiya shiya fara tuntu~ana damaganar aure.

Fim:Ke kuma ba ki tsayayin wata shawara ba kawaikika amsa masa?

Balaraba: G a s k i y ababu. Kawai ni dai ya cemaganar aure, na ce to;tunda ina son shi wace kumashawara zan je in yi? Ai inason shi.

Fim:Da ma can daga cikin’yan fim ba wanda ya ta~ajaraba nemanki da aure?

Balaraba: A’a. Ni gaskiyaba ni da wani saurayi a cikin’yan fim; da ma shi ne, tunfarkon zuwana.

Fim:Shekararku nawa dafara soyayya da shi?

Balaraba: Da Shu’aibu?Yanzu gaskiya za mu yishekara ]aya da watanni.Don shekarar 2000 na shigaharkar fim. Kuma ina shigaharkar fim na ha]u da shi.

Fim:To, ban da ’yan fim,daga waje akwai wa]andasuka neme ki da aure?

Balaraba: Gaskiya akwaida yawa. Allah ne bai nufa

ba.Fim:A Kano suke ko a

Kaduna?Balaraba: Akwai su a

Kano da kuma nan Kaduna.Akwai da su yawa.

Fim: Amma gaskiya necewa akwai wa]anda sukakawo kayan aurenki, kika yifatali da su kika ce ke sai daiKumurci?

Balaraba:{warai dagaske, akwai.

Fim: Me ya se kika cankiShu’aibu shi ka]ai?

Balaraba: Saboda na gayana da hankali, kuma yakwanta mani a rai, shi ya sa.

Fim: Ba ki yi tunaninyanayin yadda yake fitowaa fim, haka halinsa yake ba?

Balaraba: {warai. Ai ni danike tare da shi ni na sancewa ba haka halinsa yakeba. Da ya yi acting, shi newannan halin basawan yakezo mashi. Amma yanadainawa , shikenan, sai yadawo normal.

Fim:To yanzu sana’ar fimta kar~e ki, kina cin ribarta}warai. Me ya sa kika yankehukuncin barinta ki yi aure?

Balaraba: Kawai ni na gaaure shi ne martabar ’yamace. Saboda ]iya mace baaure ai shirme ne. [iya maceda aure shi ne take da daraja,kuma kowa zai ri}a ganinta

da daraja. Ka ga yanzu ]iyamace in ba ta da aure, kowa(sai) ya tashi ci matamutunci. Amma in tana daaure za a yi fargaban a cimata mutunci, za a ce ai tanada miji.

Fim:Kin ta~a samunwa]anda suka zuga ki cewakada ki auri Kumurci?

Balaraba: A k w a iwa]anda suke zuwa su kawomani zuga cewa me zan yida Shu’ aibu? Me zai ci mezai ba ni? A ina zai saka ni?A ina zai shigar da ni inzauna? Ni kuma na ce kai korami Shu’aibu zai ha}a yazaunar da ni, ina son shi. Aiso ne. In kuma }asa zaikawo ya ba ni in ci, ina iyaji}awa in sha. Saboda ni na]aukar ma raina, kuma ni naga ina son shi, ko? To dayawa ina gaya wa mutaneba}a}en maganganu, shi yasa sai aka gaji aka rabu dani.

Fim:Akwai wa]anda kikata~a ~atawa da su sabodaShu’aibu?

Balaraba: { w a r a i …Wallahi da yawa! Akwai suda yawa. Sun yi manimagana, na zazzage su.

Fim:’Yan fim ne?Balaraba: E, ’yan fim ne

mana.Fim:To shi ma daga cikin

abokansa akwai masu kushemaganar auren naku? Inanufin an ta~a sukarsawajenki?

Balaraba: A k w a i .Amma ka san abin …(dariya) sirri ne, ammaakwai da yawa.

Fim: Shi ya sani?Balaraba: Ya sani mana.Fim:To wane irin mataki

kuka ]aukar wa irinwa]annan mutane?

Balaraba: Matakin damuka ]auka shi ne, tundadai mu mun ri}e amana atsakaninmu, mu kallon kowamuke tsetse-tsetse. Wa]andaba su son al’amarin duk munsan su. Kuma tun lokacin dasuka fara kawo mana cikasa ciki, sai muka zo, in ma sungaya mana sai mu yi biris damaganarsu, mu ]aukimataki; mu muka sanmatakin da muka ]auka akansu.

Fim:Akwai wata matsalada kika ta~a fuskanta daga’yan’uwanki dangane daauren?

Balaraba: Gaskiya ni gabaki ]aya ’yan’uwana duksuna son Shu’aibu.Alhamdu lillahi, lokacin inazuwa na fa]i murna aka yi.Ni ba a kawo mani watamatsala ba.

Fim:Ke kika gabatar da

22

Balaraba:Da fim ]inMaryam naw u r i n[anzariya.

Fim:Ga shikin yankehukuncin barinsana’ar fim donki yi aure. Za kiiya tunas a n a d i y y a rha]uwarki daShu’aibu Lawan(Kumurci) harkika yankehukuncin kinason shi da aure?

Balaraba:Ni gaskiyalokacin da mukafara ha]uwa dashi, duk a cikinharkar fim ba nida wani saurayi.To, da mukaha]u da shi yanuna yana sona,ni ma na nuna

Page 24: Mujallar FIM - March 2002

Fim, Maris 2002 23

shi ga iyayenki, ko shi ya zoya gabatar da kansa?

Balaraba: Gaskiya nidai na fara zuwa na gaya mamahaifina, ya ce to yaamince. Na koma Kano nataho da Shu’aibu suka gana.

Fim:Me za ki ce danganeda zargin da ake yi wa ’yanfim cewa ko sun yi aure bazama za su yi ba, yaudara cekawai?

Balaraba: Ka san cewashi komai na Allah ne, ko?Idan Allah ya ce aure talatinza ki yi a rayuwarki, wallahisai kin yi su, ko ba a harkarfim ba. Akwai wa]anda baharkar fim suke yi ba, ammada zarar sun yi aure,wa]ansu sati biyu ya yiyawa ko wata ]aya za ka gasun fito, kuma sun yi waniauren. Akwai macen dayanzun nan ta yi aure ya figuda goma a rayuwarta,kuma ba a cikin harkar fimtake ba. Yanzu Fatin KiYarda Da Ni, ba ’yar fm bace? Tana gidan mijinta! FatiMohammed, ta fito ne kosun samu wani rikici damijinta? Haka MaijiddaAbdul}adir, ko? Duk waddaka ga ta yi aure ta fito, tohaka Ubangiji Allah yashirya mata rayuwarta.Kuma tun ran gini, ran zane.

Wa]anda suke fa]i ba suda tunani ne. Kuma suwa]anda suke fa]i, idanAllah ya nufo a kansu, su subari sai sun ga rayuwarsu ta}are ma tukuna. Ai duk]an’adam ba a gama shiryamashi rayuwa ba sai yamutu, ko? To, duk wadda take fa]i ta jira tukuna ita ma,ta ga }arewarta da duniyatukuna, in ma za ta yi watamagana ta yi. Mutane ne basu san abin da suke yi ba!

Fim: Za ki iya tuna yawanfinafinan da kika yi zuwayau?

Balaraba: Gaskiya sunada yawa, zan dai iya tunaka]an daga cikinsu.

Fim:Wane fim kika fi sodaga cikinsu?

Balaraba: Gaskiya nifinafinaina kowanne ba zance ba na so ba. Amma, kagani a cikin finafinaina,wa]anda nike masifar so,akwai Furuci, Burin Zuciya,da kuma wani fim Maryam

wanda na fara yi, da kumaJaheed.

Fim:Wane fim ne kike saran zai zama fim ]inki na}arshe?

Balaraba: Wallahi inada finafinai da dama agabana, amma fim ]in danike ganin zai zamar manina }arshe, ba mamaki,Kaci~us 2; ina ga shi ne zaizama fim ]ina na }arshe.

Fim: Akwai yarjejeniyatsakaninki da mijinki cewaza ki ci gaba da shirin fimbayan kin tare?

Balaraba: Gaskiya nikaina ba na so in na yi aurein ci gaba da fim; shi makanshi ba mu yi wannanmagana da shi ba; shi dai zaici gaba. Amma ni kamgaskiya ba na bu}atar in cigaba.

Fim:To wace sana’a za kiyi bayan kin yi aure?

Balaraba: Gaskiya ni, inzauna ma da shi kawai yaishe ni. Hankalina kwance.

Fim:Gidanku daban za kuzauna ko ko a gidansu nagado tare da iyayensa?

Balaraba: A cikingidansu ne, amma ni sashenadaban.

Fim:To kuma za ku yikiyon kare da biri ne donkada ’yan ziyara su yi makuyawa, kamar yadda wasu keyi?

Balaraba: A gaskiya, kaga ko,… Fati Mohammed, tayi aure. Akwai wa]anda keyo ]amara su same ta har]akin mijinta su ce za su cimata mutunci, ko su yi matawula}anci. To ita Fati ka gazaune take a gidan iyayenmijinta amma duk da hakaba ta tsira ba. Ka ga kumadole ne Fati ta yi magana, koba gaskiya ba? To da akecewa an yi menene an tsare,dole ne a tsare Fati.

Ni abin da nike gani, dukabin da Fati ta yi a gidantaba ta yi laifi ba. Sabodaakwai wa]anda ke zuwa suce za su ci mata mutunci,kuma ko ni nan na yi aure,gaskiya ba zan yardakowane karabiti ya zo yashigo mani gida ba. Sabodada akwai masu zuwa damuguwar niyya, su zo su ceza su ci maka mutunci. Kaga kamar ni, da a gidanmu

daban za mu zauna, saibaban shi ya ce shi bai yardaba tunda amana ce aka ba su.Ya ce ya fi so ya zo ya yigini a nan cikin gidansu yazauna. Kuma ni ma na gacewa ya dace. Saboda in bahaka ba, ka ga Shu’aibu zaiiya fita ya bar ni; yanayawan tafiye-tafiye. Wasu zasu iya zuwa su ce za su cimani mutunci.

Fim: Ya za ki ji idanKumurci ya yi maki kishiyadaga cikin ’yan fim?

Balaraba: E, to ni daigaskiya, na yarda daShu’aibu, ba ya da neme-nemen ’yan mata. Kuma niina tsammani a cikin masufim ba wata ’ya mace daShu’aibu zai samu ya ce yana so, saboda… (dariya)...saboda a gaskiya ni ba zanyarda ba ... (dariya)... Ka sandai kowace mace tana dakishi, ko ba gaskiya ba?(dariya)… Abin da gaskiyaba zai yiwu ba kenan!

Fim: Ke ba za ki yarda ya}ara aure ba kenan?

Balaraba: Ni ba zan yardaba!

Fim:To idan ba ’yar fimba ce, daga waje ya rangamota ya kawo maki fa?

Balaraba: A’a ina! Ai bazai samo ba ma. E, ba zaisamu ba, gaskiya!

Fim: To idan Allah ya}addaro sai ya yi fa?

Balaraba: Na gaya makaba zai ma samu ba. DonAllah ka share maganarkishiyar nan. Kana ~atamani rai (dariya)… Allah!

Fim: Kun yi al}awari dashi cewa ba zai yi makikishiya ba?

Balaraba: Gaskiya ni daihaka muka yi da shi. Kumana yarda da shi. Kuma donAllah ni dai ina ro}on shikada ya yi mani ki…(dariya)... kishiya! Yaddanike gudun mutuwa hakanike gudun kishiya.

Fim: Me ya fi burge kigame da Shu’aibu?

Balaraba: Gaskiya ni ayanda na sani cewa Shu’aibuba ya neman mata, kuma baya gulma, kuma ba ya wasanbanza da mata. Shi ya sa nikejin da]i, ko daga nan zuwaLondon ya je wallahi ba zanta~a tada hankalina ba.

Fim: A ina za ku yiwalima?

Balaraba: Gaskiya aKaduna, tunda a Kano ’yanHisba ba za su bari mu walaba, kamar yadda aka yi abikin Fati: saboda haka aKaduna zan yi abina hankalikwance, ba tare da ran kowaya ~aci ba.

Fim: Menene ra’ayinki akan matan da ke kasheaurensu, su dawo fim?

Balaraba: Abin da nike soin gaya masu shi ne duk dadai na san cewa Allah shi ketsara wa mutum rayuwarsa,amma su yi wa kansu fa]a.Wannan rayuwar ba ta dakyau.

Fim: To ke ga shi kin sabada samun ku]i, ga shi kumaza ki yi aure, shi kumawanda za ki aura ba mai ku]iba ne. Ya za ki yi?

Balaraba: Kamar yaddana saba samun ku]i, na sancewa da lokacin da nikebudurwata da lokacin da nayi aure, ka san rayuwata doleta canza. Lokacin da nikewaje ina samun ku]i, idankuma na shiga gidan miji, saiabin da ya ba ni. Ke macedon kina samun ku]i, ki cekuma in kika je gidan mijihaka za ki ci gaba da samu,ashe ba za ki yi zaman aurenba kenan. Idan kina samundubu ashirin dubu talatin,mijinki zai ri}a ba ki su ne?Ai ba zai yiwu ba. Da kinshiga gidan miji kawai kimanta da maganar ku]i.Muddin mace ta ce za ta yikwa]ayi, to za ta fa ha]u dawahala, gaskiya. To da nafara harkar fim kuma inasamu, kuma sai in ce idan nayi aure dole dole sai mijinaya bani? Ai ka ga ko ba za ayi zaman lafiya ba.

Fim: Daga danginShu’aibu ba wanda ya nunarashin son auren?

Balaraba: Ni dai alhamdulillahi, wallahi ’yan’uwanshisuna so na.

Fim: Me za ki ce ma masukallon finafinanki, tunda gashi za ki bar su?

Balaraba: Su gafarce ni,kuma su ci gaba da yi maniaddu’a.

Fim:To, Balaraba, Allahya ba da zaman lafiya.

Balaraba: Amin. Na gode.

Page 25: Mujallar FIM - March 2002

Fim, Maris 2002

Malam Muhammadu{aura, ]an Sarkin Fulani,shi ne mahaifin amaryaBalaraba Mohammed.Wannan shi ne karo na farkoda ya zanta da ’yan jarida akan al’amarin auren ’yar daya tabbatar da cewa ta fikusa da shi a duk cikin’ya’yansa tara. Ya tabbatarwa mujallar Fim cewa tuniShu’aibu ya biya sadakilakadan, don haka mata tazama tasa. Ya zanta dawakilinmu a gidansa da keUnguwar Kaji a Kaduna:

Fim: Baba, za mu so muji sunanka cikakke.

Malam Muhammadu: Nisunana MalamMuhammadu {aura.

Fim: To baba game dawannan aure na Balaraba daShu’aibu, menenera’ayinka?

Malam Muhammadu: E,to ni dai tunda wannan yaroya ga ’yata ya ce yana sonta, ya gama mani komai. Baabin da zan ce sai dai godiya,kuma Allah Ya sa alheri gaal’amarin.

Fim: To da ma can bawasu masu neman Balarabada aure sai shi Kumurcikawai?

Malam Muhammadu:Balaraba tana da masoya dayawa kuma masu ku]i,amma shi dai Shu’aibu shiAllah Ya }addara za ta aura.

Fim: Akwai wani bincikeda kuka yi game da shi kafinku amince ya aure ta?

Malam Muhammadu: Niba wani binciken da na yi akan shi; abin da da kawai nasani shi Musulmi ne kumaBahaushen Kano.

Fim: A ta}aice dai wannanaure ka yi farin ciki da shi.

Malam Muhammadu:{warai kuwa! Ko ba komaidai a tsakaninsu ‘kunkuru bazai nuna wa bushiya }afa

ba’.Fim: Yanzu duk shirye-

shiryen da ake bu}ata dagawajen Shu’aibun yakammala komai?

Malam Muhammadu: E,ya turo magabatanshi munkammala komai.

Fim: Ko an samu mutanenda suka ta~a kawo sukarsadangane da aurensa daBalaraba?

Malam Muhammadu: Bawanda ya ta~a kawo sukarShu’aibu wajena.

Fim: Kun sa ranar ]aurinauren?

Malam Muhammadu:Ranar Jumma’a, 15 gaMaris, 2002, za a dauramasu aure in Allah Ya so.

Fim: Ka gamsu da sana’arShu’aibu har ka ba shi auren’yar ka sa~anin mutanen dasuka ]auki sana’ar fim amatsayin iskanci?

Malam Muhammadu:{warai kuwa; ai sana’a ce,kuma su masu }yamar aurarda ’ya’yan ga ’yan fim su yihankali don kada a }i cin biria ci dila.

Fim: Shin ko ya riga yabiya sadaki ko sai ranar]aurin auren?

Malam Muhammadu:Shu’aibu ya biya sadaki,Balaraba ta zama matarshi.

Fim: Ban da sadakin

akwai wasu hidimomin dakuka ]ora masa?

Malam Muhammadu: Nidai sadaki kawai na sani,sauran abubuwa duk al’adane kuma ba ruwana da su.Ban da sadaki sai goro da yakawo muka aika wadanginmu da ke }auye.

Fim: Ba wata matsala daka samu daga ’yan’uwankagame da auren?

Malam Muhammadu:Ban samu wata matsala ba,kowa ya yi murna da auren.

Fim: Balaraba ce ta nawaa cikin ’ya’yanka?

Malam Muhammadu:’Yayana tara, Balaraba ita ceta hu]u. Amma daga cikinsuBalaraba ta fi zama ta kusagare ni. Ina ji da ita ainun.

Fim: To ya kake ji yanzukasancewar kun sha}u kumaga shi za ta yi aure ta bar ka?

Malam Muhammadu: Toai duk son da nake yi matazama ]akin mijinta shi nemafi alheri gare ni da itakanta.

Fim: Game da sana’arshirin fim da Balaraba ke yi,ba a ta~a kawo maka sukaral’amarin ba?

Malam Muhammadu:Mun sha zagi a da amma kaga da muka yi ha}uri ga shiAllah Ya rufa mata asiri tasamu miji za ta yi aure.

Fim: Daga cikin’ya’yanka za ka }ara barinwani ko wata ya gajiBalaraba a fagen shirin fim?

Malam Muhammadu: Toai ita kanta Balaraba shigartafim mu}addari ne. In AllahYa }addara cikin’yan’uwanta wani zai yi,babu abin da zan yi illaaddu’a.

Fim: A wane gari za a]aura auren?

Malam Muhammadu: Anan Kaduna za a ]aura.

Fim: To Baba kun kar~isadakin Kumurci ba tare da

]ora masa wasu lalurori ba.Wannan kun yi ne a kan binumurnin Allah ko don kunga Kumurci ba mai ku]i bane?

Malam Muhammadu: Niabin da na sani game da aureshi ne sadaki kamar yaddaaddinin Musulunci ya ce.Amma da al’ada za a bi aisai Shu’aibu ya kawobajimin sa kafin a ]auraauren, tunda Balarabajikanyar Sarkin Fulani ce.Bafillatana ce ta asali bahaye ba.

Fim: Akwai abin daBalaraba ta ta~a yi a fimwanda bai maka da]i ba?

Malam Muhammadu:Balaraba ba ta ta~a yin abinda ya ~ata mani rai ba a fim.Domin tun da ta fara dukabin da za ta yi sai tashawarce ni. Saboda hakaina yi mata godiya kumaAllah Ya yi mata albarka.

Fim: Ko ka ta~a kallonfinafinan Shu’aibu?

Malam Muhammadu: Agaskiya ni ba ma’abocinkallo ne balle in sanfinafinanshi.

Fim: Wace shawara za kaba Kumurci dagane daauren?

Malam Muhammadu:Shawara ba ta wuce in ce yayi ha}uri ya zauna lafiya damatarshi don duk mai iyalisai ya yi ha}uri. Kuma AllahYa ba shi ikon ri}e amana.

Fim: Kana da watashawara ga abokan sana’arBalaraba mata wa]anda basu yi aure ba?

Malam Muhammadu:Shawarata a nan ita ceiyayensu su ri}a yi masuaddu’a, ba su }yamace suba. Su kuma ’yan matan suyi }o}arin kare mutuncisuda na iyayensu. Kumasana’ar fim su ]auke tasana’a ce ta cin abinci. Kadasu ]auke ta matabbata.

A Kaduna wakilinmu ya waiwayi iyayen amarya a kan batun auren ’yar da suke matu}arso, ya same su cikin farin ciki tare da ]okin bikin ’yar tasu ya }arato

Da al’ada za a bi ai sai Shu’aibu ya kawo bajiminsa kafin a ]aura auren, inji mahaifin Balaraba

24

Page 26: Mujallar FIM - March 2002

Fim, Maris 2002

Wannan shi ne karo nabiyu da HAJIYA BINTAMOHAMMED ta yi hira damujallar Fim. Karo na farkoa kan al’amarin ba}in ciki dadaraddadi ne, lokacin dawasu Katsinawa suka ~ullosuka ce ’yarta tasu ce dasuka gano wai bayan ta ~acetun tana }arama. Kunkaranta labarin a Fim tawatan Agusta 2001. To, awannan karon, al’amarin nafarin ciki ne, kuma kai daganin wannan uwa tawannan kyakkyawaramaryar ka san lallai tanacikin farin ciki, dominBalaraba dai aure za ta yi. Acikin halin farin cikin neHajiya Binta ta tattauna dawakilinmu ALIYUABDULLAHI GORA II agidansu da ke Unguwar Kajia Kaduna. Bismilla:

Fim: Mama me za ki faracewa game da wannan aurena Balaraba da Shu’aibu?

Binta: To ai ni duk abin dazan ce maigidana y a riga yayi maka bayani; sai dai mutaya su addu’ar Allah yazaunar da su lafiya.

zuga ba cewa kada ki yarda’yarki ta auri Kumurcisaboda yanayin yadda akeganin fitowarsa a finafinai?

Ina addu’ar Allah ya zaunar da sulafiya, inji uwar amarya

Binta: Zuga kam dole cea yi amma mu ba mu aiki daita, dole mu kau da kai kawaimu yi masu addu’a. In kabiye ma ’yan zuga ba abinda za ka yi mai amfani.

Fim: Ke ba ki ta~ashakkun aurar da Balarabaga Kumurci ba, ganin yaddayake fitowa mugu a fim?

Binta: Yanayin yaddayake fitowa a fim bai dameni ba tunda na san ba hakayake a zahiri ba. Wasa nekawai.

Fim: Kina da watashawara da za ki bama’auratan biyu?

Binta: Shawarata a nan itace, kamar yadda suka ha]uda juna suka kuma ji suna

son juna, to don Allah su yiha}uri da juna. Shi kumamijin Allah Ya ba shi ikonri}e amana.

Fim: Wace shawara za kiba }awayen Balarabawa]anda ba su samu mijinaure ba?

Binta: To su dai yi hankalida duniya. Kuma muna tayasu addu’ar Allah Ya ba sumiji su ma.

Fim: Kina da wani sa}ozuwa ga iyayen angon?

Binta: Sa}ona kawai shine, kamar yadda muka yifarin ciki da wannan aureAllah Ya sa su ma suna farinciki da shi. Kuma don Allahsu ma su ri}a yi wama’auratan addu’ar fatanalheri.

Fim: Ya za ki bayyanazurfin farin cikinki game daauren?

Binta: Farin ciki kam ai baa magana. Tun lokacin daaka fara maganar auren nannike cike da farin ciki har gashi an zo magana ta }aretunda an biya sadaki.

Fim: Ba a ta~a kawo maki

“Mu ba muaiki da zuga...In ka biye ma’yan zuga baabin da za ka

yi maiamfani.”

’Yan aca~ar Kano za su yitseren mutuwa zuwa Kaduna?

gauraya da naskwafe(Nescafe). [aya daga aikinwuraren da ya shahara kanha]a gadagi a Kano shi newani sannanen mai shayi dake bakin kasuwar {ofarWambai kusa da masallacinidi, daidai hanyar da akeshiga cikin unguwar da kebayan ‘Festival PrimarySchool.’

Ko shakka babu bikin zaikwashi ba}i daga garuruwada dama. Har ila yau, su ma’yan kasuwar bayan fagemasu sayar da man fatur abakin titi sun ce ba za a barsu a baya ba.

Idan haka ne kuwa lallaimazauna Kaduna garinGwamma sai su yi kaffa-kaffa da yaransu don kuwaa ramar za su ga yadda ’yanaca~ar Kano ke wasan kurada babura }irar Zengchen daJengchen.

Kumurci ya samu goyonbayan ’yan aca~a da masucuwa-cuwar fetur da nigogi’yan daba sakamakonirin

WANI labari damujallar Fim taza}ulo ya tabbatar

da wani shiri da ’yan aca~arbirnin Kano masoyanShu’aibu Lawan (Kumurci)ke yi na ha]a kwamba su yijerin gwano daga Kano surankaya Kaduna domin suhalarci ]aurin aurenShu’aibu da Balaraba da zaa yi a ran 15 ga wannanwatan.

Amma kuma watamajiyar ta }ara labarta manacewa da wuya masu baburanaca~ar, wa]anda sun yi}aurin suna wurin kasada, sutsaya su yi layi. Ko shakkababu tseren yaya-da-}anen-wani za a yi, domin tuni harwani ]an taya-~era-~ari yasha alwashin ]aukar nauyinbiyan ku]in gadagi wandamasu baburan za su shadomin samun }arin kuzari.Shi dai gadagi, wani shayi neda ake ha]awa da wasusaiwoyin itatuwa sai a}walala masa madara a

rawar da yake takawa a fim,wato fitowarsa a matsayin]an daba ko wani ~ata-gari.Duk da yake a zahiri shi yarone mai kawaici, wannannau’i na al’umma sunakallonsa a matsayin waniwakili nasu a cikin harkarfim.

Wata majiya ta shaida wamujallar Fim cewa jami’antsaro, wa]anda suka ha]a dajami’an kula da tu}i a kanhanyoyi (Road Safety) da’yan sanda sun sa ido a kankwambar aca~a zuwaKaduna da kuma yaddabikin auren zai gudana.

Wani matashi na hannundamar Shu’aibu ya ce su daianguna ~angarensu ba su dawata niyya ta jawo tashin-tashina a wannan biki. Ya ce,“To, abin da muke shiryawadon farin ciki, ya za mu cemuna so a yi tashin hankalia cikinsa? Su wa]annanmutane da suke son su jebikin, ai }auna ce suke sonnunawa. Kuma mun gode.”

25

Page 27: Mujallar FIM - March 2002

Fim, Maris 2002

Daga BASHIR ABUSABE,a Gusau

A YAYIN da wasumasoya sukegudanar da

soyayyarsu ta hanyar tarhoda intanet tsakanin Amerikada Kaduna, su kuwa a Gusauta Jihar Zamfara wani abu neya faru kwatankwacin abinda yake neman faruwatsakanin A’isha Ibrahim dakuma angonta MalamaOumaten Atta. Shi daiwannan abu ana iyahangensa kamar abu na ukuda ya faru a fagen shirin fim]in Hausa, wato bayan abinda ya faru ga Saliha da Atta,da kuma Rabi Mustapha daangonta Yahaya Abubakar.Wannan abu dai shi ne aure!Su Aliyu Abdullahi Gusau,mai kamfanin shiryafinafinai na ‘Video MarkProduction’ da ke Gusau,kuma fitaccen ]an wasa, shine na farko da ya shirya fima Gusau, kuma shi nejarumin fim ]in mai suna KiYafe Ni, koda yake ya yifinafinai da dama kafin ya yinasa na kansa; sun ha]a daAuren Zamani, da BabuMaraya…, wa]anda duklittattafan daraktan hul]a da’yan jarida na gwamnanZamfara, Alh. Bashir SandaGusau, ne da aka maida fim,sai kuma finafinai irin suSalma, Sukuwa, Jaheed na 2da sauransu.

To yanzu dai Aliyu ya auritsaleliyar yarinya mai sunaAsiya Mustapha. Asiya daiba ta ta~a ganinsa ba shi mabai ta~a ganinta ba sai bayanda Ki Yafe Ni ya shigakasuwa kwanan baya. Da tagan shi a cikin fim ]in sai taji ya burge ta kuma ya yimata daidai. Kamar yadda

ABU KAMAR WASA...ABU KAMAR WASA...ABU KAMAR WASA...ABU KAMAR WASA...ABU KAMAR WASA...}aramar magana ta zama babbaLabarin yadda jarumin Ki Yafe Ni, ALIYU ABDULLAHI GUSAU, ya samu kyakkyawarmatar aure daga cikin masoyan kallonsa, kuma ba ~ata lokaci ya aure ta

Aliyu da Asiya : sun hau tsuntsun soyayya, ya kai su cikin aure

marigayi Garba Supa maigoge yake cewa, “Abukamar wasa, }aramarmagana ta zama babba!” An]aura auren Aliyu da Asiyaa garin Gulubba cikin{aramar Hukumar Gusau taJihar Zamfara a ranar 9 gaFabrairu, 2002. ’Yan fimmanya da }anana sun halarcibikin, cikinsu har dashugabannin {ungiyarFurodusoshi ta Arewa kamarsu Shugaba Hamisu Lami]oIyan-Tama da sakaren}ungiyar, AbdullahiMaikano Usman, dashugaban {ungiyarFurodusoshi ta Jihar Kano,Ibrahim Mandawari, datakwaransa na Jihar Kaduna,Adamu Bello (Ability), datakwaransu na Jihar Sokoto,M.Z. Faru, da shugaban{ungiyar ’Yan Wasa ta JiharKano, Shehu Hassan Kano,

da furodusan fim ]inDawayya, Ahmad Salihu Al-Kanawy, da furodusan AsinDa Asin kuma darakta,Magaji Sulaiman Zariya, dababban mawa}in finafinai/]an wasa kuma furodusa,wato Musbahu M. Ahmad,da sauran ’yan fim da dama.

Wannan taro ya nunayadda ’yan fim suke baAliyu Abdullahi Gusaugirma, wanda kuma shi mababban jami’i ne a cikinkwamitin zartaswa na{ungiyar Furodusoshi taArewa.

Tambayar da mutane dadama suke fa]i kafinwannan biki da kumabayansa ita ce: shin ya akayi har ma’auratan biyu sukasadu kuma har maganar takai ga aure?

To, ko kafin abin ya kai gaaure, labarin soyayyar tasu

ya bazu a cikin duniyarfinafinai kamar wutar dajitare da }arin gishiri;maganganu iri iri. Domingane gaskiyar al’amarin,wakilinmu da ke Sokoto,BASHIR ABUSABE, ya yitattaki ya je Gusau inda yasadu da Aliyu AbdullahiGusau da kuma masoyiyarsaAsiya Al-Mustapha. Shinme ya auku a tsakaninsu? Dagaske ne ita ta fara nemansashi ko a’a? Ko kuwa an yikan-kan-kan? Ya kumatambaye shi yaya yin fimyake a Zamfara? Akwaiwahala ko takurawa dagagwamnati? Yaya jama’arjihar suka amshi su masu yinfim a Gusau? Ga hirar:

Fim: Aliyu, ka }ara ba muta}aitaccen tarihinka.

Aliyu: An haife ni a nancikin garin Gusau a 1970. Na

26

Page 28: Mujallar FIM - March 2002

Fim, Maris 2002

yi karatun firamare a nanGusau, na tafi Sokoto na yisakandare. Daga nan sai na}ara gaba na tafi ‘College ofAgriculture’ da ke Zuru nayi diploma a kan kimiyyaraikin gona (Agric.Engineering). Na dawo‘Federal Polytechnic,’ {auraNamoda. Nan ma na }arayin wata diplomar a kan}ididdigar ku]i(‘Accountancy’). Bayan nagama na tafi Jami’arUsmanu [anfodio na yibabbar diploma a kimiyyarkomfuta. A halin yanzu nimalami ne a KwalejinTarayya ta ’Yanmata

(‘Federal Government GirlsCollege’), Gusau, kuma nine mataimakin mai kula dalaburare na makarantar.

Fim: Me ya ja ra’ayinkahar ka fara wasankwaikwayo bayan kaimalami ne a makarantar’yanmata?

Aliyu: Da farko dai akwaira’ayi, sannan kuma nimalami ne, kuma da maaikin malami shi ne yakarantar da halaye nagari gayara. Kuma shi wannanwasan kwaikwayon ai ka gaita ma hanya ce takarantarwa da kumanisha]antarwa. Shi ya sa na

tsunduma kaina cikinwannan harka domin infa]a]a karantarwata.

Fim: Daga yaushe ka farayin wasan kwaikwayo?

Aliyu: Na fara yin wasa a1993 da fim ]in AurenZamani, littafin BashirSanda Gusau, daraktan ya]alabarai na GwamnanZamfara; sai fim ]ina nabiyu shi ma littafinshi ne naBabu Maraya… aka maidafim; sai kuma finafinai irinsu Salma, Sukuwa, Ki YafeNi, Jaheed na 2, da daisauransu.

Fim: Wa]anda suka gafinafinanka, musamman na

baya-bayan nan, wato KiYafe Ni da kuma Sukuwa,sun ga irin matsayin da kafito. Shi ne ya sa ka buga irinwannan matsayin?

Aliyu: E to, ai ba halinaba ne, na san cewa an yi nedon fa]akarwa; a zahiri bahaka hali na yake ba. I amfriendly to people, kuma inajin da]in in zauna da jama’a,Kai ma kanka ka ga wannan.Sannan kuma ina matu}artausaya ma mata kumahalina na gaskiya ya sa~a mana cikin fim.

Fim: Mun samu labarin zaka yi aure kuma an ce fim]inka na Ki Yafe Ni shi ya

Kaduna da ’yan Gusau sukayi, fim ]in ya burge nimatu}a.” Sai ta ce ai ta sanjarumin shirin fim ]in; ta mace friend ]in mijinta ne.Bayan na tashi tafiya ne tatashi za ta rako ni, muna fitawaje sai take ce mani, “Keai ga jarumin da ya fito a KiYafe Ni can!” Sai ta nunamani shi can suna magana daabokinshi, sai tace mu je mugaisa. Shikenan sai muka tafimuka same su muka gaisakuma na nuna mashi yandafim ]in da suka yi ya burgeni. Shi ne ya ce ya gode.

Fim: Ya aka yi hargaisuwa ta yi tsawo zuwaaure?

Akwai mutanen kirki a ’yan fim – AsiyaA ~angaren AsiyaMustapha, shin me ya burgeta game da Aliyu? Me ya sata yanke shawarar aurensa?Kuma ma a ina ta san shi?Ya abin ya faru? WakilinmuBASHIR ABUSABE ya ganta a Gusau; ga yadda hirarsuta kasance:

Fim: Asiya, ]an tsakuromana tarihinki.

Asiya: An haife ni a Gusaua 1980. A Sokoto na yifiramare sannan na dawonan Gusau na yi sakandareinda daga bisani na komaGGDSS, Samaru, Zariya.

Fim: Me ya burge ki gameda Aliyu har kika yankeshawarar aurensa?

Asiya: Wannan ai waniabu ne daga Allah; Shi ne Yasa Aliyu zai zama mijinakuma ka san in ka ga mutumka ji kana son shi shikenanmagana ta }are.

Fim: A ina kika faraganinsa?

Asiya: A cikin wani fimmai suna Ki Yafe Ni inda shine ya fito a matsayin jaruminfim ]in.

Fim: Kawai sai kika ji yaburge ki?

Asiya: Ni dai tun daga nanna ji na fara sha’awar acting]in shi da kuma yanda yakegaba ]aya, sai ya buge ni.

Fim: To a ina kuka faraha]uwa kuka yi magana?

Asiya: Na je gidan wata}awata Shafa’atu GarbaGusau ina ba ta labarincewa, “Na ga wani fim a

Fim: Wane kira za ki yi mamasu hangen ’yan fim ba suda kimtsi?

Asiya: Ai ba a gane wandaba ya da kirki sai an zaunada shi. Saboda haka masuhangen rashin kimtsin ’yanfim su daina sai in ka karancihalin da kuma ri}e mutunci.A bar yin ku]in goro dominko da akwai wa]anda ba suda mutunci, to kuma akwaiwa]anda suke damutuncinsu, masu ilimi ne.Dubi dai mutane irin suSaima, yanzu haka anaboko; kuma dubi A’ishaIbrahim da irin su Aina’uAde; sannan a mazan ma gamutane irin su Zik,Mandawari, Ali da sauransu,duk suna da iliminsu.Sannan mijina ma ba jahiliba ne yana da iliminshi,yanzun haka malami ne aFGGC Gusau.

Fim: To ke ya maganarkaratun naki? Da kin yi aurekin bar shi ko kuwa?

Asiya: Insha Allahu zan cigaba da karatu bayan auren.Ina sa ran da na gama zanfa]a ko dai ABU Zariya kokuma BUK Kano – dayardar Ubangiji.

Fim: Wane kira za ki yi maangonki?

Asiya: Kiran da zan yimashi shi ne, don Allah yabar ]aukar ji-ta-ji-ta domin]aukar ji-ta-ji-ta bai dafa’ida; ina fatan zai kiyaye.

Fim: Amaya Asiya mungode.

Asiya: Ni ma na gode.

Asiya Mustaphaala}a}ai ba?

Asiya: A’a.Fim: Kin ce a cikin fim

]in ‘Ki Yafe Ni’ kika faraganinsa matsayin da ya fitoa ciki bai ba ki tsoro ba?

Asiya: A’a. Ka san abinacting, ba halin mutum bane, ana dai ba shi ne ya yiabin da darakta ya umurceshi.

Fim: Kafin ki gan shi kinzaci haka halinsa yake?

Asiya: A’a.Fim: Yaya kika samu

halinsa?Asiya: Yana da hali mai

kyau kuma halinsa yana dakirki amma watarana…(dariya).

Asiya: Kasan komainufi ne naAllah, Allahya hukuntashi nemijina.

Fim: Toy a n z u nyaushe akesa ran ]auraaure tundakomi yakankama?

A s i y a :Insha Allahub a y a nB a b b a rSallah za ayi biki.

F i m :Harkar fim]in da yakeba za tazame maki

27

Page 29: Mujallar FIM - March 2002

Fim, Maris 2002

haddasa wannan auren. Shinmeye gaskiyar lamarin?

Aliyu: Wato gaskiya ne zani yi aure kuma fim ]in dana yi na Ki Yafe Ni shi yahaifar da auren ko kuma ince shi ne media da ya ha]amu da juna saboda ban santa ba ba ta san ni ba sai bayanda ta kalli fim ]in Ki YafeNi.

Fim: Yaya abin ya faru?Aliyu: Yanda abin ya faru

shi ne na ziyarci waniabokina Sama’ila ranar wataTalata, ba zan manta ba. Harza mu yi bankwana sai nagan su ita da wata }awartamai suna Shafa’atu Garba.Suka zo muka gaisa; shi nebayan mun gama gaisuwa,kar fa ka mance da ma ba musan juna ba, sai muka zarceda hira inda take nuna manicewa ta ga fim ]ina na KiYafe Ni kuma ya yi kyau; tadai nuna mani iringamsuwar da ta yi da fim ]inda kuma yanda na burge ta.To muna nan dai ana ]antattaunawa musamman akan fim ]in, kawai kamarwasa sai na nuna mata ni tafa burge, inda har nike cemata, “Gaskiya da za a ba niwannan tsaleliyar yarinyarda na aura.” Ita kuma sai tace, “Ah, ka zo mana.” Na ce,“Allah in zo?” Sai ta kadabaki ta ce, “You’rewelcome!” Wato ta dai nunamani ina iya zuwa in shiga afafata da ni cikin masu

nemanta, domin tana damanema da yawa. Ni kumada na ji haka sai kawai na yishahadar }uda na shiga cikinmasu nemanta. Cikin ikonAllah, sai Allah ya sa ni nezan zamo zakara. Kuma dayake iyayenta masu mutuncine kuma sun san abin da akece ma fim, suka amince dani. Ga shi cikin ikon Allahbayan Babbar Sallah za a yibikin.

Fim: Yaya aka yi ka kadasauran ’yan takarar?

Aliyu: Ina ga saboda ta fi

Aliyu: Cewa ta yi gaskiyafim ]in da na yi ya burge ta.Kuma ita wannan }awar tataita ce ta kawo ta wurinamuka gaisa inda daga bisaniwani dan}on soyayya yashiga.

Fim: Ya za ka fassarawannan abin da ya faru?

Aliyu: Ah to, ka san shi soyana shiga da zaran ka gaabin da kake so. Saboda naga abin da nike so ita ma taga abin da take so shikenan,da ma shi ne fassarar so,kuma abu ne wanda Allah ya}addaro.

Fim: Me ya sa ba ka auri’yar’uwarka mai yin fim ba?Shin ko zargin da ake makuna }in auren ’yan fim yatabbata kenan?

Aliyu: Ba gaskiya ba ne;matar mutum duk inda takesai ya kalu~ota, kuma matarmutum kabarinsa. Niwannan ce Allah ya sa za tazama matata, ba ’yar fim ]inba.

Fim: Wannan na nufin nangaba za ka iya auren ’yarfim?

Aliyu: Baskiya ba nitsammani, saboda nirayuwata gaskiya ba ta matabiyu ba ce; burina guda shine in auri mata ]aya, kumana riga na samu. Insha Allahan rufe. Kuma inda a ce inada burin yin mata biyu, dagudu zan auri ’yar fim. Ah,

amincewa da ni kumagidansu duk suna amince dani, sannan uwa-uba gatantagaryar soyayya damuke ma juna.

Fim: To ita ko danginta basu kawo maganar fim ]in dakake yi ba, saboda hangenda ake yi ma ’yan fim na’yan iska?

Aliyu: Kamar yanda nagaya maka dai, ita daiyayenta sun san abin dasuke yi kuma suna da ilimi,sun san abin da ake nufi dafim, sannan kuma sun san ni

Ango Aliyu (a tsakiya) tare da abokinsa Yakubu Maigemu da Hamisu Iyan-Tama awurin dinar auren a ‘Gusau Hotel’

Amarya Asiya (a hagu) da babbar kawa Rumaisa’u a wurin dinarauren a ‘Gusau Hotel’

m a ’ a i k a c i ngwamnatin tarayyane. Wannan wasanina yi ne kawai donra’ayi da kumadomin fa]akarwa;kuma ko ba komaiita ma ai sana’a ce,ba kamar wasumutane da suka yima harkarm u m m u n a rfahimta ba.

Fim: Wato in nafahimce ka, waniabu Allah ya tashiha]awa ta hanyarfim, shi ya sa har tazo suka gaida ku?

Aliyu: E, }waraida gaske haka ]inne.

Fim: To cewa tayi ka burge ta kokuwa?

28

Page 30: Mujallar FIM - March 2002

Fim, Maris 2002

mu ba ’yan fim ba ne akeaurenmu ba?

Fim: Da ma kai can ba kada aure?

Aliyu: A’a, ban yi aure ba;wannan ne na farko.

Fim: Mu koma kanfinafinanka. Shin butulcinda ka yi ma Habiba a cikinKi Yafe Ni, ba ka tunanin zaija maka matsala, mutane suri}a tunanin haka halinkayake?

Aliyu: Masu hankali ba zasu yi irin wannan tunanin basaboda ni ba halina ba ne,kuma sai wa]anda sukajahilci abin za su yi irinwannan tunanin. Kuma itaHabiba ma tana ]aya dagacikin manyan aminaina acikin film industry.

Fim: Amma wasu za su yitunanin ka yi irin wannanhalin a cikin Sukuwa…

Aliyu: (katse hanzari) Aia Sukuwa ba soyayya na yiba. Kuma ko a nan maHafsat is my close associate,haka shi ma Sani Danjantunda duk su na yi ma }afarungulu. Abin da ya kamataa gane shi ne a cikin fim abinda darakta ya umurce ka kayi shi za ka yi.

Fim: Ga shi a Zamfarakusan ku ne na farko da kukafara shirya fim. Wa]anneirin nasarori kake ganin kuncimmawa?

Aliyu: Farko mun samugoyon bayan mutane dawa]anda suka rubuto kumada wa]anda suka yo tarhoko wani abu makamcinhaka. Mun gode }warai.Muma mun shiga sahunsauran jihohin irin su Kano,Kaduna, Sokoto da sauransua cikin harkar fim. Kuma a~angaren gwamnati munsamu goyon baya tundalokacin da za a }addamar dafim ]in Babu Maraya… taba da gudunmuwar ku]i. Shifim ]in Babu Maraya... taraba ma jami’anta.

Fim: Ka tuna mani wasuna hangen cewa yin fim aZamfara yana da wahalasaboda ana shari’a a garin,amma ga shi har kana cewagwamnati ta ba ku taimako.Ya abin yake?

Aliyu: Lokacin da za mu}addamar da fim ]in,Gwamna ya yi mana hu]ubakuma ya ja mana kunne akan mu tabbata duk fim ]inda za mu yi bai sa~a mashari’a ba, kuma ya ba mutaimako na N100,000,mataimakinshi kuma ya bamu N30,000. Sannan kumagwamna ya ba {ungiyarFurodusoshi ta Zamfarabashin mota bas, wato}ar}ashin shirin ‘Zapa LoanScheme.’

Fim: Kenan duk ji-ta-ji-tar

da ake ya]awa game da fima Gusau ba gaskiya ba ce?

Aliyu: Ba gaskiya ba ce.Ba wanda ya hana mu yinfim a Zamfara kowane iri nein dai har bai sa~a ma shari’ada al’adunmu ba.

Fim: Kwanaki an ce ankama ka. Shin gaskiya ne?Kuma me ya sa aka kamaka?

Aliyu: Wallahi ba gaskiyaba ne, ni ma haka na yi ta jinmaganganu irin wannan.Babu wanda ya kama ni,kuma fim yana nan muna yi,ga sabo ma za mu fara yi.

Fim: Me ya sa ake cewaan kama ka?

Aliyu: Ni wallahi ban saniba. Ka san abin da ya faru?Ranar nan ina dawowa gidasai na iske mutane sun zogidanmu wai sun zo jaje waiYarima (GwamnanZamfara) ya sa an kama nisaboda fim. Kawai sai ga nina diro kamar daga sama.Wannan duk labarin }anzonkurege ne. Tsakaninmu daYarima sai godiya.

Fim: [azu na ji ka ceYarima ya ba {ungiyarFurodusoshi Jihar Zamfarabashin mota. Shin kuna da}ungiyar furodusoshi ne?

Aliyu: E, bayan an kafa taArewa mu ma sai muka kafatamu }ar}ashin jagorancinAlhaji Abdullahi [an

Gusau. Ni nemataimakinshi.

Fim: To ya za a yi ku biyabashin?

Aliyu: Muna nan ma munkusan biyan bashin. Yaddaake yi kuwa shi ne aiki akeyi da motar (fasinja), dukwata mu ba gwamnati waniabu mu kuma ware ma motawani abu, sauran canji mujefa aljihun }ungiya.

Fim: Wa]anne irinmatsaloli kuka fuskantayayin gudanar da wannanfim?

Aliyu: Mhm! Matsalar’yan wasa na kan gaba,saboda sai ka ga an ha]a’yan wasa amma sai wasu su}i zuwa. Haka aka yi tafama. Sai kuma wata matsalada muka ha]u da ita bayanmun gama ]aukar fim ]inmu har ba}in da mukagayyato daga Kano daKaduna duk sun koma; saikawai aka ]auki rushes ]inda muka yi (kaset ]in da ke]auke da hotunan bidiyonfim kafin a gyara su) dazaton sabon kaset ne aka tafiwani aiki da shi. Ba donmun farga ba da an yi manabaya-ba-zani. Lokacin daake je amso rushes ]in sauraka]an ya fara ]aukar da shi.Ka ga da an yi mana asara;sai mun sake gayyato ’yanwasan kenan.

Fim: Daga }arshe wanekira kake da shi?

Aliyu: Ina kira ga masushirya fim gaba ]ayansu dasu bar hassada da munafuncidomin wannan duk shi kehaddasa ci-baya a wannanharka. Kuma ina kira gamasu ku]i da su tsundumasu saka jari a cikin harkarfim saboda samun ci-gaba.Haka ita ma gwamnati tataimaka kamar yadda wasugwamnatoci, musamman nawasu }asashe irin Indiya ketaimakawa. Ina godiya gaGwamnan Zamfara, Alh.Ahmed Sani Yarima, saikuma surukaina da sukaamince suka ba ni ]iyarsu dakuma yadda suka fahimciyadda harkar fim take, damutane irin su MaryamBamalli, Maryam AhmedMaiwada, duk a Zariya, saikuma Shafa’atu GarbaGusau, duk ina mi}a godiyata musamman a gare su.

Amarya tare da kawayenta suna cashewa a wurin dinar auren a ‘Gusau Hotel’

29

Page 31: Mujallar FIM - March 2002

Fim, Maris 2002

B U K U K U W ADaga MUHAMMED NASIRa Kano

IN ban da Abubakar mijinMaijidda Abdul}adir(wanda shi ma ba ]an

fim ba ne, ’yar fim yakeaure), babu wani mutumguda ]aya da za a iyanunawa a ce darakta ne, kofurodusa ko ]an wasa,maka]i ko mawa}i a wurin]aurin auren fitacciyarzabiyar finafinai RabiMustapha. An ]aura aurenRabi da wani ma’aikacingwamnatin tarayya mai sunaYahaya Abubakar a ran 16ga Fabrairu a cikin unguwarSoron [inki kusa da gidanSarkin Dawakin Tsakar Gidaa Kano.

Rabi, wadda ta zamayarinyar bangon mujallarFim a watan jiya, ta ri}a bida kanta a ofisoshindaraktoci da furodusoshitana raba masu katingayyatar ]aurin aurenta.Wakilinmu ya samu nasakatin ta hannun Rabi kumaya halarci wurin da misalin}arfe 1:20 na rana. Da maan rubuta cewa za a ]aureauren da }arfe 1:30 ne. Ba adai ]aura auren ba sai }arfe2:15, amma har 2:30,lokacin da anguna suka barwurin, ba a ga wani ]an fimya je wurin ba.

Wani abin ]aure kai gawannan muguwar halayya ta’yan fim ita ce sun fi yi wamawa}a mata wannanrashin zumunci. Domin ko]aurin auren Zuwaira,fitacciyar mawa}iyar fim,’yan fim ]in da suka jewurin ba su fi a }irga su dayatsun hannu ba. Yawancinwa]anda Fim ta nemi dalilinda ya sa suka }i halartar]aurin auren wannanyarinya wacce ta ba dababbar gudunmawa gaha~akar shirin fim na Hausasun rantse cewa wai ba susani ba, kuma ba a gayyacesu ba. Ga shi kuwa wannanmujallar wadda sukankaranta ta ruwaito labarinauren sosai.

Wani mutum cewa ya yishi dai bai ji da]in ganincewa ’yan fim ba su je]aurin auren ba. “Abinkunya ne,” inji shi. Kumawani daga cikin tawagar da

Abin kunya a ]aurin auren Rabi Mustapha...

BABU [AN FIMKO [AYA!

ta zo daga Abuja ya cewa yayi, “Ai gaskiya ba hujja bace ]an fim ya ce sai angayyace shi ]aurin auren’yar fim kafin ya je. Asheabin babu ha]in kai kenan.”

Wani matashin furodusamai suna Mohammed BashirBala ya bayyana cewa shidai tabbas ya san da ba tunauren amma bai santakamaimen ramar daurawaba. Batun kati kuwa yace baa ba shi ba. Duk da haka yace ya ji an ce “wai katingayyata ne ya yi }aranci.

“To shin su wa]anda aka bakatin me ya sa ba su je ba?”inji shi, ya kuma }ara dafa]in, “Wa]anda aka bai wakatin gayyata ba su kyautaba.”

Wani bincike da wannanmujallar ta yi ya tabbatar dacewa an sami }aranci katingayyatar ]aurin auren.

Angon Rabi, Yahaya, yashaida wa mujallar Fimcewa ya gode Allah tunda yaida nufin al}awarin da ya]auka na auren Rabi. Da akatambaye shi ko akwai wani

jawabi da zai yi wa jama’adon ganin Rabi za ta yi masukewa, sai ya ce, “E, na sanzan raba su da Rabi, toamma kuma na sanmasoyanta ne ko in cemasoyanmu. Ina yi masugodiya da ba su ha}urisaboda na ]auke ta.”

Wasu daga cikin abokanango da suka halarci wurinsun ha]a da MustaphaMohammed Inuwa, JibrinWada, Alh. Hamisu, ASPDanjuma, Alh. Yawale daHamza Rilwanu.

RASHIN halartar]aurin auren RabiMustapha da ’yan

fim maza suka yi bai hanatakwarorinsu mata halartar

walimar da aka shirya aranar ]aurin auren ba. Anshirya gudanar da walimarda misalin }arfe 8:00 na darea dandalin matasa na Sani

Abacha da ke Panshekara,Kano, amma saboda dalilintsaro sai mafi yawan ’yanmata suka nuna rashin yardada wurin. Daga bisani sai

30

Rabi Mustapha da mijinta Yahaya Sadiq

... Walimar auren ta }ayatar,an yi ruwan ku]i

Page 32: Mujallar FIM - March 2002

Fim, Maris 2002

B U K U K U W Aaka dawo Gidan [anhausada ke kan Titin Sokoto, cikinrukunin gidaje naNassarawa.

Daga cikin wa]anda sukari}a kai-da-kawowa donganin kimtsuwar bikinakwai jaruma A’ishatuSmally da kuma Hadiza Fijowadda ita ma ’yar wasa ceda ta yi aure a cikin 2001.

Ana fara gabatar dashagalin sai AleebabaYakasai da MuntariKwanzuma suka faragabatar da ka]e-ka]e, kumaMudassir {assim da SadiSidi Sharifai suka fara yin

wa}o}i. Ba su da]e dafarawa ba sai ango daamarya suka iso cikin watamota wacce ke kewaye dawasu jami’an tsaro gudabiyu da aka taho da su dagaAbuja.

Bayan ango da amaryasun zauna sai aka gabatar daFatima Ibrahim (Tasallah),Hauwa Ali Dodo, MaijiddaAbdul}adir da mijintaAbubakar (anda yana ]ayadaga cikin abokan ango) dakuma sauran abokan ango

suka zauna a layin da angoda amarya suke.

An ci gaba da raye-raye dawa}e-wa}e inda suShu’aibu Idris (Lilisco), Liloda Sani Musa (Mai Iska)suka yi rawar Sa’a Ta FiGata.

Wannan biki ya nunaAbida Mohammed tana da]imbin masoya. Lokacin data shigo tana wa}ar nan tafim ]in {auna, an baibayeta ana ta she}a mata ku]i.

A wurin, mutane da dama

BABBAN abokinangon RabiMustapha, Mustapha

Mohammed Inuwa Mafara, yayi jawabin godiya ga jama’amusamman saboda yadda akakar~e su hannu biyu-biyu agidan amarya da kuma yadda’yan fim suka halarci walimartasu. Ya nuna jin da]in raye-

ZA MU {ARA AUREN ’YAR FIM, inji abokin angoWasu mutane suna ta tambaya: shin Tasalla ce ko Biba?

31

sun yi ta}aitattun jawabai.Fatima Ibahim ta nuna farincikinta kuma ta yi wa jama’aban-gajiya. Ta gode wa dukwanda ya samu damarhalartar walimar da mawanda bai samu dama ba.

Rabi amarya kuma tanuna jin da]in auren da ta yi,ta kuma gode wa jama’a. Tanemi yin dogon bayani,amma da ta fara yin rawarmurya kamar za ta yi kuka,sai ta ha}ura ta zauna. Takuma yi wa jama’a wa}arbankwana inda ta rera wa}arGidan Duniya.

raye da wa}e-wa}en da akashirya domin taya su murna. Acikin raha ya nuna cewa dayardar Allah sai sun sakedawowa Kano sun }ara auren’yar wasa. Wata majiya cewa tayi a bisa dukkan alamu ]ayadaga cikin abokan angon yanason Fatima Ibrahim (Tasalla).Haka kuma wani daga cikin

abokan ango ya ri}a fa]a abayan fage cewa yana son watafitacciyar ’yar wasa. Mutane awurin sun yi zaton ko HauwaAli Dodo ce domin an ga wanina ta ~arar da ku]i a kanta.Lokacin da take yi wa suMudassir li}i, shi kuma sai yaje yana yi mata. An ]aukitsawon lokaci yana zazzaga

mata ku]i har mutane suka ri}amamaki.

Wani abin farin ciki da yafaru a wurin shi ne kyautargudummuwar ku]i da Rabi tasamu daga hannun AleebabaYakasai har N20,000. ’Yanwasa da dama dai sun je bikinwanda aka tashi kafin 11:00 nadare.

A RANAR Asabar, 2 gaMaris (ranar da akafara buga mujallar Fim

ta wannan watan) aka gabatarda bikin Gala na BabbarSallah a filin wasan }wallon}afa na ‘Ranchers Bees’ da keKaduna. Bikin ya samuhalartar ’yan kallo a}alla dububiyu. Kuma ya }ayatar,musamman saboda yadda akafara lafiya aka kuma }arelafiya.

Kamfanoni biyu, ‘Ya-Kareem Ventures’ na Zariyada ‘Film & VideoConsultants’ da ke Kano, sune suka shirya bikin.

An fara gudanar da bikin damisalin }arfe 10 na safe, indaaka fara da gabatar da ’yanwasan da aka gayyato dagaKaduna, Zariya da Kano. Baa gayyato ’yan wasa na wasugaruruwan ba.

Daga Kano, wa]anda suka

zo sun ha]a da Shehu HassanKano; Hauwa Ali Dodo,Halima Adamu Yahaya, LadiMutu-Ka-Raba, AminuShariff Ahlan, Bappa Yaro,Auwalu Marshal, M.D.Mukhtar, da Hajara Abubakar(Dum~aru). Ban da ’yanwasa, akwai furodusoshi dadaraktoci da dama.

Abin da ya rage wa aya za}ishi ne wasu ’yan wasa dadama wa]anda jama’a ke songani ba su halarci bikin ba,domin ko dai sun tafi Nijarwurin wata Galar a can kokuma ba a gayyace su ba. Dukda haka, wa]anda suka zo ]insun }o}arta matu}a wajen}ayatar da jama’a wajenwa}o}i da ka]e-ka]enfitattun finafinai. Wa}o}insun ha]a da na finafinanImani, Karama, Maina,Sururi, da Hauwa.

Masu shirya bikin sun

}o}arta wajen tanadar damatakan tsaro a bikin, indaaka baza sojoji, ’yan sanda da’yan banga a wurin. Sai daiduk da haka wasu ~ata-garinmatasa sun kusa na}asaHauwa Ali Dodo sa’ilin daake wucewa ta tsakiyarsu tareda ita zuwa tsakar fili, sukadam}e ta don su ta~a ta, harsuka ji mata rauni a hannu.“Ban ta~a shan wuyar Gala bairin wannan,” haka waniwakilinmu ya ji Biba ]in tanaambatawa.

Shugaban furodusoshinJihar Kaduna, Adamu Bello(Ability), wanda ya jagorancishirya bikin, ya bayyana wamujallar Fim dalilin shiryawannan taron a lokacin damutane ba su tsammani, watokwanaki bayan Sallah. Ya ce,“Irin wannan biki, kusan in ceshirya shi a kowane irinyanayi ba laifi ba ne, domin

muna so ne mu tabbatar wa dajama’a cewa mun sadaukar darayuwarmu a kan wannansana’a, musamman ganinyadda shirin fim ke }arakar~uwa ga jama’a. Kumakada mutane su yi tsammanindon samun ku]i muka shiryaGalar, a’a, wannan Gala munshirya ta ne kawai don munisha]antar da masoyanmu.”

A nata ~angaren, HalimaAdamu Yahaya, wadda ita cejami’ar kamfanin ‘Film &Video Consultants’ a bikin,cewa ta yi, “Ni jin da]inakawai shi ne, duk Galar da akeyi ba wadda aka yi aka tashilafiya kamar wannan.”

Taron ya tashi da }arfe 5 nayamma. Daga nan ’yan kallosuka soma watsewa, su kuma’yan fim suka koma masaukia otal otal na cikin garinKaduna, wasu kuma sukakoma Kano da Zariya.

Galar Babbar Sallah a Kaduna: Anburge, kuma an yi lafiya

Page 33: Mujallar FIM - March 2002

Fim, Maris 200232

R A H O T O

Gobara daga kogi a Jos!Me ya haifar da zubar da jini a taron ’yan fim na Jihar Filato?

Waziri Zayyanu Sani Muhammed Sani

Shirya Finafinai ta Arewareshen Jihar Filato, inda akacire wasu jami’an }ungiyaraka sa wasu. Daga cikinwa]anda sauyin ya shafa harda Aminu Hudu Alma,wanda aka bai wa mu}aminmataimakin shugaba. Kafinhaka shi ne mai bincikenku]in }ungiyar. Ya mayegurbin Sani MuhammedSani wanda shi nemataimakin sakatare-janarna {ungiyar Furodusoshi taArewa.

Wannan sauyi ya faru nea taron da }ungiyar tagudanar a ran Lahadi, 17 gaFabrairu, 2002.

Har yanzu dai fitaccendaraktan nan WaziriZayyanu ne shugaban}ungiyar, kuma UsmanIbrahim yana nan amatsayinsa na sakatare.

Bayan wannan kuma, dayake }ungiyar ta }unshi tadaraktoci da ta furodusoshida ta ’yan wasa, an gudanarda wasu za~u~~ukan a}ar}ashin reshen kowace}ungiya. A reshen daraktocian za~i Magaji Mijinyawa amatsayin shugaba, yayin da

Sadiq Hung ya zamasakatare. Su kumafurodusoshi, MalamShamsuddeen suka za~a amatsayin shugaba, sa’annanAli Jasawa yakesakatarensu. A reshen ’yanwasa, Alhaji Mustapha yazama shugaba yayin daIbrahim Achimota yakesakatare.

Kafin a kai ga yin wannantaron kuwa, an yi }o}arinyin taron a wata rana can abaya, sai dai wani ru]ani daya faru a ]akin taron ya satilas sai a ran 17 ga wata akayi shi. A waccan ranar dai angama karanta ajandar tarosai jami’in hul]a da jama’ana lokacin, Shamsuddeen,ya ba da shawarar cewa “yakamata a yi amfani dawannan dama a sasantasa~anin da ke tsakaninAminu Alma da SaniMuhammed Sani.”

Majiyarmu ta tabbatar dacewa rufe bakinShamsuddeen ]in ke dawuya sai Alma ya nuna cewashi fa bai yarda a tayar damaganar abin da ketsakaninsa da Sani ba. Ganin

Daga ISMA’IL M. ISMA’ILAa Jos

AN gudanar da wasusauye-sauye a cikinshugabannin da ke

jagorancin {ungiyar Masu

jama’a sun matsa lamba, saiya fusata ya tashi zai fitadaga zauren taron. Amma kokafin ya }arasa bakin }ofatuni har Sani ya fusata dawasu kalamai da aka ce shiAlma ya fa]a, ya garzaya yacakumi rigar Alma ya kaimasa naushi a fuska.

“Wallahi ya yi min naushizai kai bakwai,” inji Almalokacin da wani wakilin Fima Kano ya tunkare shi donjin tabbacin rikicin.

Mujallar Fim ta ganocewa Alma ya garzayaofishin ’yan sanda na ‘C Di-vision’ inda ya shigar dakukan abin da ya faru. Sukuma ’yan sanda ba su yiwata-wata ba sai suka tafi]akin taron cikin farin kayatare da shi, suka yo awongaba da Sani. Sai dai kumawasu gaggan ’yan fim naJos sun yi }o}arin kashewutar inda Waziri Zayyanuya kar~o belinsa.

Sani Muhammed Sani,wanda tsohon wakilinmujallar Fim ne na Jos, daAminu Alma sun samumugun sa~ani ne tun canbaya lokacin da Alma ya

shirya yin wani fim ]insamai suna Gobara Daga Kogi.Sani ne daraktan fim ]in.Tun ba su gama shirya fim]in ba sa~ani ya shigatsakaninsu, wanda ya haifarda dagulewar zumunci atsakaninsu, abin da kowa yasani a fagen fim na Jos.

Alma da Sani dukkansu’yan wasa ne kumafurodusoshi. Alma ya fito afinafinai irin su {u]iri,Huznee, da Hali. Sani kumashi ne daraktan finafinaikamar Girgizar {asa, wandabai fito ba tukuna. DukkansuJasawa ne, sai dai kumasukan yi wa Kano zaman je-ka-ka-dawo.

To, ya aka yi sa~aninsu yadagule haka? Me ya yi zafi?Menene gaskiyar abin dakowannensu ya }ullaci]ayan da shi? Ta wace hanyaJasawa za su iya sasanta su?

Duk za ku ji amsoshinwa]annan tambayoyin dagabakin Sani Muhammed Sanida Aminu Hudu Alma, tareda shawarwarin wasu ’yanfim na Jos, a mujaallar Fimta watan gobe. Ku biyo muku sha labari.

Page 34: Mujallar FIM - March 2002

Fim, Maris 2002

L A B A R A I

|arayi sun yi wa furodusa }ar}afDaga ASHAFA MURNAIBARKIYA a Kano

“Wai me kuka shakka, ga ni gaku,[auri kuka shakka ko kashewa?Don ni ga irin mugun nufina,Da a ba ni kujerarMakka kyauta,Gara in ishe mai jikka tamaninYa yi sagoooo, ya sadda kai}asa,In ga hawaye suna zubo masaDuk da na koko bai da rannanSai dangi sun ba shi ramce,Sai in ji kamar na taki Arfa,Duk wani da]i ya }ume ni...Don uban wani ya komamatsiyaci.”– Gambu, “Wa}ar |arayi”

WANNAN wani baiti nedaga cikin wa}ar

Muhammadu Gambu mai wa}arbarayi inda yake nuna farin cikiidan ~arawo ya mayar da “ubanwani matsiyaci.” Irin wannankuwa ta faru ga wani sabonfurodusa da ya da]e yana shiryawasu finafinai guda biyu a Kanoamma har yanzu ba su fito ba.

Abin tausayi, matashin, SaniUba Idrisu (Rasha) yana daf dafara samun ribar wahalar da yasha sai ~arayi suka dirar masa.Satar ta ]aure wa jama’a dadama kai ganin cewa ba a ]aukikomai ba sai duk wani abu daya shafi finafinan, wato MugunBaki da kuma Guguwa.

Mujallar Fim ta ji ta bakinfurodusan wanda ya daure yabayyana duk yadda abin ya faru.A cewar Sani, “Na tashi damisalin }arfe 7 na safe, na shigacikin gidanmu sai na gamahaifina da matansa guda biyuda wasu daga cikin }annena sunyi tagumi suna salati.

“Da na tambaye su me yafaru, sai aka shaida min cewajiya da dare (Asabar, 2/2/02)~arayi sun hauro gidan kuma basu saci kayan mutanen gidan basai kayana. Kuma kayan da akasata wata babbar jaka ce damuke zuba kayan fim ]inmu aciki.”

Da aka tambaye shiabubuwan da ke cikin jakar, saiya fara lissafi:

1. Akwai master copy originalna Guguwa; akwai rushes na fim]in Guguwa kaset 8 a ciki;akwai second master guda uku;

“Za su kai N225,000. Wani abinkuma ba zai lissafu ba.”

Ya }ara da cewa bayan abinya faru sai suka je ofishin ’yansanda da ke Shara]a a ran 4 gaFabrairu suka kai rahoto. ’Yansandan sun ba su damar cewa dazarar sun ga wani abu ]aya dagacikin wa]anda aka sace masu,to su gaggauta sanar da su.

Wakilinmu ya tambaye shi baya jin abin kamar cinne aka yimasa don a ta}aita shi? Sai Saniya ce, “Ha}i}a ni na san dukwanda ya saci wannan kayan toyana da masaniyar inda akeajiye kayan.” Sai dai kuma harlokacin da ake hira da shi baizargi kowa ba, kuma wanda ya]auka ya bar shi da Allah.

Su dai wa]annan finafinaiguda biyu duk ba su fito ba. Toza mu iya cewa sunayensu sunbi su kenan? Allah ya tsare gaba.

Daga WAKILINMUa Kaduna

SAU da yawa, ~arayi sukanyi sata a gidajen mutane ne

da daddare, lokacin duk an yibarci, mutum bai san inda kansayake ba. To amma wata sata daaka yi a gidan mawallafinmujallar Fim a garin Kaduna,Malam Ibrahim Sheme, ta bakowa mamaki domin da ranakata aka yi ta, a tsakanin bayan}arfe 12 zuwa kafin }arfe 1.

Yadda abin ya faru shi ne atsakiyar watan Janairu, 2002, damisalin }arfe 12 daidai saimai]akin Ibrahim ta lura cewalokacin tashin makarantar’ya’yansu mata su biyu da kemakarantar reno (nursery) ya yi,ga shi kuma mai ]auko su (wata}anwar su Ibrahim) ba ta dawodaga makarantar sakandare maizaman kanta da take ba. Ga shiduk sauran mutanen gidan ba sunan. Don haka sai ta yi sauri tashirya ta tafi ]auko yaran. Tadawo gidan da misalin }arfe 1na rana.

Tana zuwa sai ta ji an kulleget ]in gidan da wani abu dagaciki. Da aka bu]e }ofar da tsiya

sai aka ga ashe ~arayi ne sukakai farmaki gidan. Sun fasagilashin taga, suka kuma ~allofamfon da ke tsakar gida sukayi amfani da shi wajen gagga~e}arafunan da aka giggita a tagardon tsaro, suka shiga cikin falo.

A falo, sun ]auki na’urori irinsu bidiyo da rikoda da dutsenguga da fitilar lantarki(rechargeable lamp) dasauransu. Sun shiga ]akunakuma, suka kwashe dukkanakwatunan da matar Ibrahim ke

adana kayan sawanta da na yarada sauransu. A ta}aice, in banda kayan da ke jikin mutanengidan, da kuma kayan wanki dasuke zube a wani ]aki, ba su barko }yalle a gidan ba.

A daidai lokacin da aka yisatar shi Ibrahim Sheme yanakan hanyarsa ta komawaKaduna daga Kaano.

An lura cewa ~arayin sundiro ne daga wani ]an fili a kankatangar gidan ta baya. Ammaabin mamaki shi ne yadda sukayi satar suka gudu babu wandaya gan su, musamman da yakelayi ne wanda mutane suke bisosai. Kuma an tabbatar dacewa in dai ba da ha]in bakinwasu daga cikin matasan da kegidan ma}wabta ba, da wuya akwashe kayan nan masu yawahaka in ba a mota ba. An yizargin cewa ~arayin ba wasu bane illa nigogin unguwa (matasamarasa aikin yi) wa]anda sunyawaita a unguwar.

Mutane da dama sun yi wamawallafin mujallar da iyalinsajaje, wasu kuma suka aiko dasa}onnin jajen, musamman mamembobin guruf ]in ‘FinafinanHausa’ na intanet. Kai, wasu hargudunmuwar ku]i suka yi wamatar ta Ibrahim Sheme.

Sani Uba (Rasha)

... Sun washe gidan mawallafin mujallarFim da rana tsaka

akwai trailer guda hu]u; akwaifosta ta Guguwa inci 9; akwai}ananan fosta (handbills) guda1,000; akwai rasi]in shiga

sinima guda 3,000; akwairushes na fim ]in Mugun Bakiguda 5; akwai master copy naMugun Baki (original); akwaisecond master guda 2; akwaifosta mai 9 ta Mugun Baki;akwai rijista ta }ungiyar KanoFilmmakers a ciki; akwai rijistata MOPPAN a ciki; akwai ba}arjaka wadda MOPPAN ta rabawa furodusoshi a ciki; saitakardun makaranta(credentials) tun daga firamarehar zuwa Polytechnic duk ansace; sai wata ba}ar jaka waddakayan }annenane a ciki (tufafi);ita ma sun saci kayan fim ne;akwai ID card na MOPPAN aciki; akwai }ananan hotuna daaka ]auka a wurin ]aukar fim]in daban-daban.”

Bayan duk ya gama wannanlissafi, an tambaye shi ko zai iyayi wa kayan }iyasi? Sai ya ce,

Ibrahim Sheme

33

Page 35: Mujallar FIM - March 2002

Fim, Maris 2002

L A B A R A I

{ungiyar karanta Fim ta soki lamirin gasar {ungiyar karanta Fim ta soki lamirin gasar {ungiyar karanta Fim ta soki lamirin gasar {ungiyar karanta Fim ta soki lamirin gasar {ungiyar karanta Fim ta soki lamirin gasar ArewaArewaArewaArewaArewaDaga Bashir Yahuza,a Katsina

IRIN kwarjini da tasirin damujallar Fim ke }ara yi ga

makaranta sai }ara bayyana take yi. A wannan karon a birninDikko ne wasu matasa suka kafa}ungiya ta karanta mujallar.

Matasan, wa]anda sun bu]eofishin wucin-gadi a unguwar[aki Tara a Katsina, sun yitattaki zuwa wajen wakilinmu,inda suka sha alwashin }arabun}asa martabar mujallar,musamman wajen ba da goyonbaya, tare da mi}a shawarwariga hukumar gudanarwarta,domin ta ci gaba da ]aukaka, dawayar da kan al’umma game daharkokin finafinai.

Shugaban }ungiyar na ri}o,Malam Zahraddin Umar [aki-Tara, ya fayyace irin ayyukan da}ungiyar za ta dingagudanarwa. A cewarsa, za suri}a kai ziyara ga kamfanoninshirya finafinai dake arewacin}asar nan, kuma za su ri}a bafurodusoshi shawarwari don suri}a inganta finafinan Hausayadda za su ri}a bun}asa da]aukaka al’adunmu daaddininmu. Kuma ya ce sunajinjina ga mawallafin mujallar,Ibrahim Sheme, tare da sauran]aukacin ma’aikatanta.

Shi ma sakataren }ungiyar nari}o, Malam Aminu AhmedMuhammed, ya ba da goyonbaya ga mujallar, tare dagamsuwa da kasancewarta. Akan haka ne ma ya shawarcimawallafin mujallar da ya cigaba da ba wasi}un makarantamuhimmanci domin hakan zai}ara dan}on zumuncitsakaninsu da mujallar.

{ungiyar ta makaranta Fimsuna nuna sha’awa cewa nangaba ka]an su ma za su farashirya fim da sunan }ungiyar.Sai dai sun yi kira ga attajiranKatsina da su tallafa masudomin su sami damar shigasahun masu wayar da al’umma.

A wani }arin bayani dashugaban ri}on }ungiyar ya yi,ya yi kira ga duk masu karantamujallar da ke Katsina, maisha’awar shiga }ungiyar yatuntu~e su a ofishinsu na wucin-

}ungiyar sun nuna takaici da~acin rai ga masu gudanar dagasar finafinai na Arewa(‘Arewa Films Awards’),musamman saboda }in bai wamujallar Fim wata kyauta tayabawa duk kuwa da cewamujallar na taimakawa sosaiwajen bun}asa harkokinfinafinai. Kuma sun kusheyadda aka }i bai wa marigayiMansur {walli kyautar tunawada gwarzon mamaci. Kamarkuma yadda suka ce, masushirya kyautar ba su bishawarwarin masu kallon fimba, duk kuwa da cewa an aikamusu da ]imbin wasi}u a kanhaka. ’Yan }ungiyar sun yi kiraga kamfanin ‘Arewa Awards’]in da a nan gaba su bara’ayoyin masu kallomuhimmanci, don a samudaidaito.

Daga ALIYU A. GORA IIa Kaduna

WANI sabon furodusa dagaSuleja, Jihar Neja, wanda

ya kammala shirin fim ]insakwanan nan mai suna Firdausi,Alhaji Idris Tankon Baraka, yayi kira ga furodusoshinArewacin }asar nan da su bamujallar Fim cikakken ha]in kaida goyon baya.

Furodusan, wanda kumashi ne shugaban kamfanin‘Zuma Rock Movies’ da keSuleja, ya ce hakn ya zama dole,musamman idan aka yi la’akarida irin gudunmawar da mujallartake bayarwa wajennisha]antarwa tare da fahimtarda jama’a kan abin da duniyarfinafinai take ciki.

Alhaji Idris ya yi wannan kirane yayin da ya kai ziyara aofishin mujallar Fim da keKaduna a ranar Alhamis, 27 gaDisamba, 2001.

Alhaji Idris ya }ara da jawohankalin furodusoshi da cewaya lura da yawa daga cikinfurodusoshi sukan yi wahalar

banza, domin a cewarsa, saimutum ya kashe ku]i ma}udaiwajen shirya fim, amma ]anabin da zai kashe ya tallata fim]in a mujalla sai ya gagare shi.Maimakon haka, ya ce sai ka gafurodusa ya zama almajiri, yana

ro}on wani ya]an saka masatalla a fim ]in sa.

Daga }arshe,ya sake jawoh a n k a l i n’ y a n ’ u w a n s afurodusoshi dacewa, “Ina kira gas a u r a nf u r o d u s o s h i’yan’uwana, damu yi tunani, murungumi mujallarFim kamar yaddata rungumisana’armu, takuma du}ufawajen ya]amartabar da kecikin sana’ar, donwa]anda muke yidominsu sufahimce mu.”Haka kuma ya yi

Malam Aminu AhmedMalam Zahraddin Umar

Wasu furodusoshi sun maidakansu almajirai, cewar furodusa

gadi da ke [aki Tara. Nan gabaka]an, da sun kammala shirye-shirye, ’yan }ungiyar za su kai

ziyara a kamfanin mujallar Fimdomin sada zumunta dama’aikatanta.Daga }arshe, ’yan

Alh. Idris Tankon Baraka

kira ga masu kallon finafinai dasu ri}a rubuto ra’ayoyinsugame da duk wani fim da sukakalla, domin wannan zaitaimaka wa furodusa ya sankuskuren da ya yi a fim ]insadon ya gyara a gaba.

34

Page 36: Mujallar FIM - March 2002

Fim, Maris 2002

Karrama mawa}a da maka]an fim ya yi daidai

BASHIR Nayaya([anmagori) wanda

shahararren ]an wasa ne, yabayyana jin da]insa tare dayabawa kan karrama mawa}a damaka]a wanda mujallar Fim tayi a watan Janairu. Ya ce,“Wannan abu da kuka yi zai }arafahimtar da ’yan wasa su ganecewa ko shakka babu maka]ada mawa}a suna daga cikinwa]anda suka taimaka harkarfinafinan Hausa ta bun}asa harta kawo wannan mataki da ta kea kai.”

[anmagori, wanda tsohon

– inji [anmagorida kuma ku]in da AlhajiMustapha Mohammed (MalamMamman, [anhaki) ya samu,sai Malam Bashir Nayaya ya ce,“Duk wani wanda ya taimakawa [anhaki da wani abu, toAllah ya saka masa da alheri.Amma kuma ita mujallar Fimce musabbabi domin ita ta yitunanin karrama shi”.

A }arshe ya yi fatan kadamujallar ta karaya a shekara maizuwa, ta }ara himma ta karramawasu daban. Malam Bashir Nayaya

]an wasan gidan talbijin ne, ya}ara da nuni inda ya ce, “Kumaka ga ba don irin wa]annankarramawar ba, to wani har yagama yayinsa ya daina ba zaisan an gode masa kangudunmuwar da ya bayar wajenciyar da finafinan Hausa gababa.”

Ya ro}i hukumomi da}ungiyoyi da su yi koyi da abinda mujallar Fim ta yi domin}ara fito da martabar fim a fili.

Da ya koma kan karramawa

WANI kofur ]in sojamai sha’awar karantamujallar Fim da

kallon finafinan Hausa ya jahankalin ma’aikatan mujallarda su }ara zage damtse kada sununa gajiyawa ko kasala wajenaiwatar da ayyukansu.

Kofur Gambo SulaimanHa]ejia, wanda yana tare ne dabarikin sojojin kai ]aukingaggawa (‘MilitaryContonment’) da ke Ikeja,Legas, ya yi wannan garga]i nelokacin da ya kawo ziyaraofishin mujallar da ke Kano aran 14 ga Fabrairu.

Ya yi bayanin cewa mujallarFim tana kawo abubuwan ciyarda harshen Hausa gaba da kumakare martabarsa, musamman awasu ~angarorin }asar nan.Kofur Gambo ya nuna farin cikida cewa ko shakka babu suHausawa mazauna Legas sunaalfahari da mujallar,musamman kuma irinsu masusha’awar kallon finfinan Hausa.

Cikin bayanan da ya yi, sojanya shawarci furodusoshi dadaraktoci da su ri}a tacekurakurai a cikin finafinansukafin su fitar da su kasuwa. Yakuma yi ro}on su rage yingaggawa wurin shirya fim dafito da shi. Ya kuma bu}acidaraktoci da su ri}a horas dasababbin ’yan wasa kafin a ri}asaka su cikin finafinai. A }arsheya ro}i ’yan wasa mata da su}ara kare mutuncinsu da

Ban da gajiya, ban da kasala!– garga]in Kofur Gambo ga Fim

Ya zo Kano ne domin’yan’uwansa su shaida cewa shi

Cpl. Gambo S. Hadejia

martabarsu. “Kuma su tuna bafinafinan Inyamurai suke yi ba,Musulmi ne su kuma Hausawamasu kyawawan ]abi’u”.

Shi dai Kofur GamboSulaiman yana ]aya daga cikinmasu yawan rubuto wasi}u nashawara ga mujallar Fim. Ko acikin mujallar watan Fabrairuakwai wasi}arsa da aka buga ashafi na 9. Kuma ya sha bugawaya a babban ofishin mujallarna Kaduna don neman labarinhalin da ’yan fim ke ciki.

Sojan mai igiya biyu, ]anshekaru 33, ya shiga aikin sojashekara 14 da ta gabata (1989).

da iyalansa suna lafiya bayanha]arin fashewar bamabamai]inn nan da ya auku a barikinsojojin da yake kwanan baya.Ya ce ha]arin bai shafe shi sosaikai tsaye ba, “sai dai wani ]an~angare na bangon ginin gidanda nake ciki ne ya rushe”.

Abdu Haro ya ba’yan }wallo kyautar‘Dum~aru’Daga BASHIR YAHUZAa Katsina

A RANAR Jumma’a, 18 gaJanairu, 2002, da misalin

karfe 3:30 ne al’umma suka yidandazo a babban filin wasannina Katsina domin kallon wasan}arshe na gasar }wallon }afawadda Sardaunan FuroduoshinArewa kuma ]an MajasarTarayya da ke wakiltar }anananhukumomin Mashi da Dutsi aJihar Katsina ya shirya. Gasarwadda aka yi wa la}abi da‘Gasar cin kofin }wallon }afata Hon. Abdu Haro Mashi,’ tasamu halartar }ungiyoyin}wallon }afa da dama daga}ananan hukumonin biyu.

An ]auki lokaci ana fatatawaa gasar. A wasan }arshe, anbuga }wallo ne tsakanin}ungiyar ‘lone Stars ‘A’ ta garinMashi da kuma wacce ke

wakiltar {aramar HukumarDutsi, wato ‘ShargalleHighlanders’.

Wasan ya samu halartarmanyan ba}i. an gayyato Hon.Alhaji Ghali Umar Na’abba,Kakakin Majalisar Wakilai amatsayin babban ba}o, wanda

L A B A R A I

Alh. Abdu Haro Mashi

35

Page 37: Mujallar FIM - March 2002

Fim, Maris 2002

ya samu halartar bikin tare dawasu fitattun ’yan majalisa irinsu Hon. Abubakar Sadiq’Yar’Adua. Haka kuma akwaiGwamnan Jihar Katsina, AlhajiUmaru Musa ’Yar’Adua damataimakinsa Alh. TukurAhmed Ji}amshi, da kakakinMajalisar Dokoki ta jihar, Alh.Sani Sai’du Fago, da sauranhamsha}an mutane.

Daga }arshe an tashi gasar daci 5 da 3 bayan an tashi kunnendoki 1 da 1 , daga bisani aka yibugun daga-kai-saigola, inda’yan Shargalle suka ci hu]u,Mashi suka ci biyu, wato wasaya tashi 5 da 3 kenan.

Kafin a raba kyaututtuka,wani fitaccen ]an wasankwaikwayo, Salisu Kakis, yashirya wata wa}ar maraba maida]i inda ya rera ta a gabanjama’a kuma ta nisha]antar damutane sosai.

A jawabinsa na dalilin sanyawannan gasa, Alhaji Abdu HaroMashi ys ce ya shirya wannangasa ne saboda bun}asa jinda]in matasa da wasannin

motsa jiki, domin kuma }ara dan}onzumuta a tsakanin al’ummonin }anananhukumomin da ke maza~arsa.

Sardaunan masu shirya finafinan kumaya nuna cewa duk shekara zai ci gaba da]aukar nauyin gudanar da wannan gasa.Kuma ya sha alwashin kafa babbar}ungiyar }wallon }afa ta }ashin kansa,wacce za a za~o }wararrun ’yan wasatalatin daga }ungiyoyin da suka shigagasar wannan shekarar.

{ungiyar da ta zo ta ]aya, wato‘Shargalle Highlanders’, sun amshi kyautarmota }irar bas, wacce ake ma la}ani da‘Dum~aru,’ tare da kofi da wasu }ananankyaututtuka na }wallaye da sauransu. Itakuwa }ungiyar da ta zo ta biyu, wato‘Mashi Lone Stars ‘A’ ta samu kyautarmanyan babura guda biyu da kofi da saurankyaututtuka }anana daban-daban. Ta ukukuwa, wato }ungiyar ‘Mashi Lone Stars‘B’, ta samu kekunan hawa guda 18 da}aramin kofi da wasu sauran }ananankyaututtuka.

An raba wasu kyaututtukan daban-daban ga babban ba}o Hon. Ghali UmarNa’abba, da Gwamnan Katsina da AlhajiLawal Kaita, da kuma kakakin majalisarKatsina da sauransu. An tashi bikin lafiya,kowa na fa]in Allah maimaita mana.

L A B A R A I

KAMAR yadda sana’arshirin fim ta zama ruwan

dare a Jihar Kano, kwanci tashiKaduna ma ta bi sahu, dominkusan duk sati yanzu ana samunsabon furodusa.

[aya daga cikin wa]annansababbin furodusoshi, AyubaShu’aibu wanda ake yi wala}abi da Chikago, yanzu hakaya kammala ]aukar shirin fim]insa mai suna So Masifa Ne,wanda aka fara ]auka aka kumakammala a cikin garin Kaduna.

Da wakilinmu ya nemi sanindalilin shigowar Chikago afagen shirin fim, sai ya kadabaki ya ce, “Na farko dai nada]e ina sha’awar kallonfinafinai na Indiya da naTurawa, tun kafin ma a fara yinna Hausa.

“Da na fara kallon na Hausakuma sai suka shiga raina ahankali, har na fara tunaninyadda ni ma zan zama ]ayadaga cikin wa]annan ’yan fim.A hankali Allah ya yi manibu]i, domin sana’ar fawa nikeyi, to kuma sai fa]uwa ta zo

daidai da zama, domin akwai wani abokinawanda shi ya da]e da shiga cikin shirinfim. Na nemi shawara har aka kai ga nayanke shawarar shirya fim na }ashinkaina.”

Malam Ayuba ya }ara da cewa ba yashigo sana’ar fim ba ne don ya rainasana’ar fawa, ya ce ya shigo harkar nekawai don sha’awar da yake yi wa fim tunlokaci mai tsawo da ya wuce. Daga }arsheya ce sana’ar fawa ba zai ta~a yin watsi daita ba saboda shirin fim, saboda ita ya sami,ita ya iya.

‘Ba zan iya barin fawa basaboda fim’

Ayuba Shu’aibu (Chikago)36

SUNA: Rahma Abdullahi S.SUNAN RANA: JummaiSHEKARU: 18GARIN HAIHUWA: SokotoMATSAYIN KARATU: Sakandare (Habmass)AURE: BabuFINAFINANKI: Sukuwa (Zilai)WANDA KIKA FI SO: SukuwaKAYAN SAWA DA KIKA FI SO: MaterialsGWANAYENKI: Hindatu Bashir, Sani Danja,

Fati Moh’d, da Abida Moh’dABIN KYAUTA DA KIKA FI SO: Frame da

mujallar FimHALAYEN NAMIJI DA KIKE SO: Gaskiya da

ri}on amanaKIN TA|A HA[UWA DA MAI WANNANHALIN?: A’aINDA KIKA FI SON ZIYARTA: Saudiyya da

AmerikaABIN DA KIKA FI SON KARANTAWA: Al}ur’aniABIN DA BA KI SO: {aryaABIN DA BA KI SO A YI MAKI CIKIN JAMA’A:

TozartawaKIN IYA MOTA?: EKAYAN LAMBU DA KIKE SO: Tuffa, ayaba,

mangwaroME KIKE SO KI ZAMA?: Lauya

Rahma Abdullahi

MMMMMUUUUU S S S S SANANANANAN ’Y ’Y ’Y ’Y ’YANANANANAN W W W W WASAASAASAASAASA

RahmaRahmaRahmaRahmaRahma

Page 38: Mujallar FIM - March 2002

Fim, Maris 2002

Daga ABUBAKAR MAIHOTOa Gusau

A GUSAU, babban birnin JiharZamfara, mutane da dama sunji da]in yadda gwamnatin jihar

ta yi }o}arin rufe gidajen sinima.Hasali ma dai gwamnatin ta sayesinimomin domin masu sinimun susami abin da za su ri}a juyawa dominciyar da iyalinsu. Bayan haka gwamnatita mayar da sinimun cibiyoyin harkokinaddinin Musulunci. Sinimar nan maisuna ‘Rio’ an mayar da ita wajen koyontajwidin Al}ur’ani, sannan cikin watanazumin Ramadan an gudanar da tafsirinAl}ur’ani mai girma a cikinta. Hakakuma ya faru ga wata a garin Gummi,sannan ]aya sinimar mai suna ‘WorldWise’ da ke Tudun Wada, Gusau, itama bayan nazarin Al}ur’ani da ake yia cikinta ana raba wa malamanmakarantun allo buhunan hatsi da zasu ciyar da almajiransu a kowane wata.

A ganmin al’ummar jihar, wa]annan

RAHOTON MUSAMMAN

A ZAMFARA BABU SAURAN

Labarin yadda gwamnatin Jihar Zamfara ta fito da dokarrufe gidajen sinima bayan ta }addamar da Shari’a

sinimu wurare ne da yara suke koyonmiyagun ]abi’u kamar sata, shan giya,shaye-shayen ganye, koken, caca, zinada liwa]i. Ba ma wa]annan kawai bababban abin da ya fi tayar wa mutaneda hankali shi ne, a daidai lokacin daake gudanar da fim za ka ga wa]ansusun tashi suna kewayawa suna ro}onAllah suna ha]a Allah da darajarAnnabi Muhammadu (SAW) cewaAllah ya ~atar da sinimar ko Allah yaaiko da wani irn bala’i. Irin wannanro}on yana tayar wa mutane da hankali;wasu, komai irin son da suke yi ma fim,dole su fita daga sinimar. Wasu ma daga}arshe sukan yi wa kansu fa]a su barshiga sinima baki ]aya.

A ranar da aka yi bukin bu]e sinimara matsayin cibiyar nazarin Al}ur’anikwanan baya, malamai da dama sun yijawabai. [aya daga cikinsu, MalamLawali Mai Shari’ah, godiya ya yi gaAllah (SWT) ganin cewa babu wanigida da ake ce ma sinima a fa]in JiharZamfara a halin yanzu, saboda lokacinda gwamnati ta ba da damar a rufesinimomin wani ya ce masa ya yi ba}incikin hakan. Bayan haka, MalamLawali ya ro}i Allah da Ya shiryar da

Alha. Ahmad Sani YarimanBakura, Gwamnan Jihar Zamfara

‘Rio Cinema’: Daya daga cikin manyan sinimun Gusau, yanzu cibiyar nazarin Alkur’animai tsarki ce

duk wani wanda ya ta~a ~atancizuwa gare shi ko kuma Shari’arAllah. Sannan ya }ara da cewaduk wani wanda ya ta~a yimasa laifi ko ya yafe masasaboda jin da]in da yake yi awannan rana.

Shi kuwa Dr. Atiku BalarabeZawiyya Gusau, cewa ya yiyana ]aukar wannan ranakamar ranar da aka zo fathulmakkati, watau ranar daMusulunci ya ci garin Makka,wanda yake tabbas cewa an kai}arshe ruwa sun kai }wari,Manzon Allah (SAW) ya ce:“Babu hijira bayan cin Makka”saboda Musulunci ya kai indabai shakkar kowa. Ya }ara dacewa, “Alhamdu lillahi,wannan gida kowa ya san irinmuninsa, kuma yanzu kowa yasan irin girman nasarar da akasamu na kasancewar cibiyarkarantar da karatun Al}ur’ani

37

Page 39: Mujallar FIM - March 2002

Fim, Maris 2002

a wannan wurin.”A nasa ~angaren, Malam Wakkala,

kwamishinan addini, farawa ya yi da cewa:“Allah (SWT) ya ce: ‘A yi tun}aho dafalalar Allah da rahamarSa, za a yi farin cikida shi duk ya fi wani abin duniya da mutumzai tara’”. Ya ce abin da ya sa ya fa]iwannan maganar shi ne yana tunanin bayaa lokacin da gwamnan Jihar Zamfara ya haumulki ba da da]ewa ba ya sa shi cikinkwamiti don ganin an aiwatar da Shari’aha lokacin suna mitin sai suka kawo maganarsinima, sai wani bawan Allah ya tashi yanata fa]a, ya ce masu suna da hankali kuwa?Ko Sardaunan Sokoto ai bai rufe sinimominba, ballantana Ahmad Sani Yarima, ai babuwanda ya isa ya zo ya rufe wannan sinima.Kwamishinan ya }ara da cewa, a lokacinda suke tunani irin wannan ’yan’uwaMusulmi na wannan unguwar, wa]andasuka shirya wannan wa’azi da ake yi, wataua ranar bu]e sinima a matsayin cibiyarnazarin Al}ur’ani, ya same su ya sanar dasu maganar da ake yi ta rufe sinima, ya ceyakamata su nuna goyon bayansu game damaganar Shari’ar Musulunci a jihar. Ya cemasu lallai shari’ar Musulunci ya tabbata aga cewa mutanen da za su nuna makwamitin shari’a cewar lallai suna so su gaan rufe sinima ta koma gidan shari’a,wa]annan matasa sun rubuta wasi}u fiyeda 300 kan cewar suna son ganin an rufesinima. Yin hakan shi ya kawo dole aka rufesinima saboda al’ummar jihar sun ce ba subu}atar sinima a jihar.

Kwamishinan ya }ara da cewar bayanhaka ranar 6 ga watan Oktoba, kafin a}addamar da shari’a ya iske Gwamnan jiharya ce masa, “Allah ya taimake ka! Allah yataimake mu a wannan jahar wannanal’amarin shari’a da Allah ya sa ka jagorantaan rufe gidajen karuwai an rufe gidajen giyatun kafin ranar }addamar da Shari’a alhalihar yanzu akwai wa]ansu abubuwa gudabiyu manya-manya wa]anda ya kamata asaye su.”

Gwamna ya ce, “Menene?”Sai Kwamishinan ya ce masa, “Na farko

gidagen sinima.”Nan take Gwamna ya ce ya je ya ba da

sanarwar cewa kafin ranar 27 Oktoba, 1999,duk inda sinima take a fa]in Jihar Zamfaraa rufe ta gaba ]aya. Bayan an rufe suGwamna ya sa aka kirawo masu sinimunaka zauna tare da su bisa teburin shawaraaka ce masu, “Maganar sinima an rufe, babuja da baya; don haka me kuke ganin yakamata? Ku zo ku ba da ha]in kai a sayesinima.”

Da farko sun fara jayayya. KwamishinanAddini ya }ara da cewa, “Abin mamaki, acikin wannan maganar akwai wasu ’yanwannan unguwar ta kusa da ‘Rio Cinema’wa]anda suke ganin don me za a rufesinima, an yi shisshigi an yi }wace! Allahya shiryi wa]annan mutane ya gafartamasu!” A cewar kwamishinan, akwai dagacikinsu wa]anda suka jagoranci masu

sinima, suka same shi har gida da wa]ansu’yan kyaututuka da ku]i, suka ce in yanaso za su ba shi miliyoyin ku]i kan cewar abar su su ci gaba da harkar sinima a JiharZamfara. Kwamishina ya ce masu, “Munaro}on Allah da ya tsare mu kada mu yi riddabayan mun sa gaba kan imani.” Ya ce alokacin da yake ba mai girma gwamnan

watan mai daraja Gwamna zai zo wurindomin taron bu]e kwas na tajawidinAl}ur’ani,” sannan ya wuce ]aya sinimarda ke Tudun Wada. Za a bu]e wata cibiyara garin Gummi nan gaba ka]an inshaAllahu.

Daga }arshe ya yi addu’a ga GwamnanJihar Zamfara tare da sauran Musulmin

Taron kaddamar da Shari’a a Gusau

wannan labarin sai gwamna ya buga teburya ce, “Wallahi! Wallahi! Babu maganar jada baya game da maganar rufe sinima aJahar Zamfara!” Ya ce a kira su masusinima, ya ce ko su sayar da sinima ko kumaan rufe ta har abada.

Lokacin da aka kira su suka fa]i abin daza a ba su, nan take gwamna ya ce a ba su.“Cikin taimakon Allah,” inji Kwamishinan,“duk fa]in Zamfara aka rufe sinima.” Ya}ara da cewar zai yi wa jama’ar JiharZamfara wata bushara kuma wa]annansamarin da suka shirya wannan wa’azi sukace suna son a mayar da wurin da ake sa~onAllah ya zama wurin da ake fa]in }alaAllahu }ala Rasulu. A lokacin da Ma’aikatarAddini ta je wurin Gwamna ta sanar da shiabin da jama’a suke so, nan take sai yayarda. Bayan haka Kwamishinan ya yi kiraga jama’ar Musulmin jihar kamar yaddakwanan baya aka yi wa’azi a wannanunguwa aka ce daga rannan a bar kirantaBakin Sinima sai dai {ofar Yarima, yanaro}on ’yan’uwa Musulmi su yardar manida a ri}a kiran wannan sinima da sunan‘Yarima Islamic Centre’ da izinin mai darajaGwamna nan take jama’a suka ]aukikabbara suna, “Mun amince mun amince!”

Sannan ya juya zuwa ga Gwamna yasanar da shi bu}atar Musulmi saboda sunason cibiyar ta yi daidai da sunan wannanunguwar “da wannan jihadi da ka yi ba donkai ba sai domin muna ro}on Allah (S.A.W)ya saka maka da dukkan alhairinsa.” Sannanya ce kamar yadda aka taru aka yi wa’azi awannan wurin duk kowane wata za a taru ayi wa’azi a wurin insha Allahu. Kuma yace, “Ranar Asabar mai zuwa a wannan

38

jihar.Bayan tasowar Gwamna sai jama’a suka

]auki kabbara, “Allahu Akubar! AllahuAkubar!” A lokacin da ya zo kusa da turunmagana sai alaramma ya yi bismillah, yajawo surar Izaja’a nasurullahi har}arshenta.

Sannan Gwamna ya yi kabbara ukukamar yadda ya saba yi a duk inda ya jewajen taro, ya kori She]an ya yi bisimillah,ya yi yabon shugaban manzanni tare daiyalansa da sahabbansa. Daga nan ya yisallama ga jama’a ya ce ya yi godiya gaAllah (S.A.W.).

Gwamna ya ce lallai lokacin da ya tasoyana }o}arin ya gaya wa alaramma cewarya fara da wannan sura sai ya manta ammacikin ikon Allah sai ga ta Allah ya sa yafara da ita. Yarima ya ce wannan wani ikonAllah ne, sannan ya ce abin da ya sa ya so afara da wannan surar shi ne mutanenwannan unguwar babu abin da za su yi saisu gode wa Allah (S.W.A). Kuma wannangida da aka mayar cibiya ta Musulunci yakasnace mutanen wannan unguwar yara dasun taso idan ana neman mahaddata a garinGusau a samu dubu saba’in sun fito awannan unguwar. Jama’a gaba ]aya saisuka ]auki kabbara. Sannan Yarima ya }arada cewa wurin zai zama wurin da za a ri}akoyon tajawidin Al}ur’ani da hadisanManzon Allah (S.A.W).

Gwamnan ya ce: “Allah (S.W.A) yace:‘Huwallazi arsala Rasulahu bil huda wadinil ha}}i liyuzhirahu aladdini kullihiwalau karihar kafirun” sada}alLahulazeem. Yarima ya ce, “Wannan aikin baaikinmu ba ne, aikin Allah (S.W.A) ne.”

Page 40: Mujallar FIM - March 2002

Fim, Maris 2002

A kafiri yamutu duk daaikin da ya yiwa Musulunci

see p. 92 of Empire magazineANTHONYO u e e nO e a k a

shi ne sunanshahararren maishirya finafinaikuma da rubutasu, wanda kumaya }ware wajenzane-zane dasuka dangancifinafinan dayake shiryawa.

Da wuya kace ba ka sanAnthony Queenba, sai dai idanba ka ta~akallon fim ]innan mai sunaO u m a rMukhtar: Lionof the Desert ba,wanda aka nunay a d d aal’ummar }asarLibya suka ya}iItaliya lokacinda take }o}arinmallake ta donyi mata mulkinmallaka. ShiA n t h o n yQueen, shi ne yafito a matsayindattijo UmarM u k h t a r ,wanda malaminallo ne wandaya jagorancijama’arsa wajenyin fa]a da

Italiyawa duk kuwada kasancewar shi dajama’arsa ba su damuggan makamai nazamani irin naabokan gabarsu.

Shi dai wannanshahararren ]anwasan, an haife shi aran 21 ga Afrilu, 1915a garin Shiwaha a}asar Meziko.Mahaifinsa ]an kuwa]an asalin }asarAiland (Ireland) ne,ita kuwa babarsa ’yarMeziko ce. Wata ranasai }anwar babarsa ta]auke shi zuwa garinLos Anjales da keAmerika tare da waniyaro da ta ]auka amatsayin ]anta. To,daga nan ne faAnthony ya shigarayuwa mai tsanani,ya ri}a fa]i-tashiwajen ya ga cewa yazai ya samu damarrayuwa shi da]an’uwansa. Ya yisana’o’i da dama. Acikin sana’o’in da yagwada kuwa awannan lokaci sunha]a da farauta dadambe. To, daga nanne ya tashi dagawannan zuwa wanigari suka hau kwale-kwale irin namutanen Japan, mai]an inji. Isarsu garin

Rayuwar Anthony Queen,jarumin shirin Umar Muktar

DagaDagaDagaDagaDaga

ABDULLAHI IBRAHIM DOGUWABDULLAHI IBRAHIM DOGUWABDULLAHI IBRAHIM DOGUWABDULLAHI IBRAHIM DOGUWABDULLAHI IBRAHIM DOGUWAAAAA

39

Page 41: Mujallar FIM - March 2002

Fim, Maris 2002

ke da wuya sai ga wani furodusa nafinafinan amerika (Hollywood) yananeman mutum mai siffar Indiyoyin Dajidomin ya fito a matsayin Indiyan Dajia wani fim da shi wannan furodusanyake son shiryawa. Kwatsam, sai yaha]u da Anthony. Da ma kuma ya yikama da Indiyan Daji. Kawai sai ya yimasa magana shi kuma sai ya yarda.Anthony Queen ya tsinci kansa kamara mafarki a harkar fim. Wannan abu yafaru a shakarar 1963. Sai dai daga farkowannan furodusa ya so ya kore shisaboda tsayinsa ya yi yawa, to ammahakan ba ta faru ba. Ya ha}ura ya cigaba da shi a hakan.

Wannan shi ne farkon shigarsa harkarfim. Ya yi wasa a finafinai har guda 130,sa’annan ya shirya nasa na kansa gudabiyar. Wa]annan finafinai su ne NicolasRay, Elylazan, John Storges, FedricaFileleny, Davidsen, kuma gaba ]ayawa]annan finafinan da ya shirya gudabiyar sai da suna zama daga cikinmanya-manyan finafinai a duniya.

Anthony Queen ya kasance yana sonmore rayuwa kuma yana son matasosai. Ya yi auri-saki, don ya auri matauku, amma matan da ya yi mu’amalata banza tare da su suna da yawan

Anthony Queen a tsakanin ’ya’yansa da jikokinsa

gaske. Yana da shekara 21 ya fara yinaure, kuma ba a da]e ba ya sake tadomin binciken wata matar. Matarsa tafarko, Catherine, ’yar furodusan nan neda ya fara sa shi a fim. Ta haifa masa

’ya’ya biyar amma ]aya ya mutu atafkin yin kurme (swimming pool). Aduk lokacin da ya tuna da wannan abu(mutuwar ]an) yana ba}in ciki baka]an ba.

Anthony Queen a cikin wani fim

40

Page 42: Mujallar FIM - March 2002

Fim, Maris 2002

Matarsa ta biyu mai sunaYolanda ta haifar masa’ya’ya uku kuma ta nemi yasake ta, saboda kishin datake yi yana mu’amala damatan da ba nasa ba, ammahar sai da suka kai shekara30 tare sannan suka rabu.

A lokacin da Anthony yakai shekara tamanin 80 saiya kai ziyara }asar Meziko,jama’ar }asar suka yi masatarya irin ta ban grima kai kace shugaban wata }asa ne yazo. Kuma a wannan shekararne ya tara ’ya’yansa suka]auki hotuna irin na tarihi.

Wannan tsohon zaki yakasance yana sha’awar manzaitun da motoci manya-manya. D yana yaro ya shatunanin ko zai kai matsayinmanya-manyan mashahuranmasu shirin finafinai da akasan su a duniya. Sai ga shiburinsa ya cika a lokacin daya kai shekaru 80 a duniya.Anthony ya kasance mutummai son yara }anana,musamman ma sababbinhaihuwa.

Matarsa ta uku kuwa ita ceCarthy kuma ita ce matarsata }arshe a cikin jerin matanda ya aura. Kafin ya aure taita ce sakatariyarsa, suka yi

auren a lokacin tana dashekaru 35.

Ya yi fim ]insa na }arshea cikin 1998 mai sunaIntiqam. Ya fa]a da bakinsacewa, “Ina shirya finafinaine saboda na sami ku]i to,sauran saboda na samu dukaabin da nake so amma kumaba dama domin iyalina sunason walwala da sha}atawa.”

Kada mu manta, ban daUmar Mukhar, AnthonyQueen ne ya fito a matsayinjarumin fim ]in nan maisuna Arrisala: The Message,inda fito a matsayinSayyidina Hamza. Hakakuma ya taka muhimmiyarrawa a fim ]in Lawrence ofArabia, wanda shi malabarin rayuwar Larabawane.

Saboda wa]annanfinafinai da ya yi wa]andasuka danganci tarihinMusulunci, lokacin da yamutu a cikin 1991 yana dashekaru 86 mutane da dama,musamman a duniyarMusulmi, sun ]aukaAnthony Queen shahidi newanda ya musulunta kafinya mutu. To a gaskiya yamutu a matsayin kafiri ne,akasin yadda ake zato.

Ashe gemu ba ya hana wasa? A cikin hotunan da kewannan shafin, Anthony Queen ne yake cashewa. Rawatana daga cikin abubuwan da ke ba shi sha’awa kumayana takawa a duk lokacin da bukata ta motsa masa

41

Page 43: Mujallar FIM - March 2002

Fim, Maris 2002

Fim: Fatima, bari mu farada jin ta}aitaccen tarihinki.

Fatima: E, to, assalamualaikum. Ni dai ka sansunana Fatima Abubakar.Tarihina kuma, ni ruwa biyuce: mahaifiyata Bafillatanace, mahaifina kumaBazazzagi ne. To ka ji, niBahausa ce kenan ko, ata}aice.

Fim: Za mu so mu sanshekarar da aka haife ki, dakuma garin da aka haife ki.

Fatima: Gaskiya an haifeni a cikin Kaduna, a Malalicikin Low-cost, a shekarar1983.

Fim: Labarin makarantafa?

Fatima: Makaranta, na yitun daga firamare ta Malaliinda na dawo Badarawa na}arasa. Na je sakandare bangama ba, na tsaya a aji hu]u,amma insha Allahu zan cigaba har in }are.

Fim:Wace sakandarenkika yi?

Fatima: G.G.D.S.STafawa-|alewa, a nanKaduna.

Fim: Harkar fim ce ta sakika tsuke karatun ko kuwa?

Fatima: A gaskiya baharkar fim ba ce ta fitar dani, wata matsalar ce tadaban, wadda ba dole ba nein bayyana ta.

Fim: Ya aka yi kika shigoharkar shirin fim?

Fatima: E, to, alhamdulillahi, gaskiya abin da ya sana shigo harkar fim shi ne,na ji ina da ra’ayi na kalloda yawa, ina kuma karantamujalla da makamatansu.

Me ake ciki game da shirin fim a Kaduna?

SHIRIN FIM A KADUNA

SHIN me ya sa duk furodusan da ya tashi shirya fim a Kadunasai ya garzaya Kano ya kwaso ’yan wasa, ya manta da nagida? ’Yan wasan Kaduna ba su kai na Kano }warewa bane? Ko ba za a iya tallata su har su ma a san su ba? Shin ’yanwasan Kaduna sun gamsu da wannan ]abi’a tafurodusoshinsu?

A cikin ’yan watanni ka]an da suka shige, an samuyawaitar aikin shirya fim a Kaduna. Wannan ya sa wasu

matasan ’yan fim sun fara kunno kai don a dama da su awannan harkar. Su waye su? A cikinsu akwai daraktoci da’yan wasa wa]anda suke ganin idan har aka ba su dama, toza su nuna wa duniya cewa su ma fa ba }ashin yadawa ba nea fagen shirin fim. Wakilinmu ALIYU ABDULLAHI GORAII ya ]an kewaya gari inda ya sadu da wasu wa]anda akeganin za a dama da su a bana, amma fa idan masu abin sunamince. Ga su:

’Yan wasan Kano ba su fi mu ba– Fatima AbubakarSai suka cusa mani ra’ayin

son shirin fim, har na shigo.Fim: Da wane fim kika

fara?Fatima: Fim ]in da na fara

yi shi ne Tasiri na kamfanin‘Nas Fim Production,’Kaduna. Na biyu shi ne Jini[aya na kamfanin ‘Al-Yusuffas Film Production,’Kaduna,’ sai Hikaya da Illa.

Fim: To, kamar yadda kilakin jin wasu mutane na cewa’yan fim ’yan iska ne, ke dakika shigo kin tarar dahakan?

Fatima: (dariya) Ka sanmutane ba su taruwa suzama ]aya. Amma a harkarfim in ka ga mutum yanaiskanci, to shi ya sa kanshiiskanci zai yi.

Fim: Zuwa wane lokacikike sa ran barin sana’arfim? Ko ke ma shiga sojanBadakkare kika yi masa?

Fatima: Gakiya na ]ibarmata lokaci, ban maida tasana’a ta dindindin ba.Saboda ba ni ke da rayuwataba, ba ni ke da kaina ba.Insha Allahu, in Maisama yayarda, in lokacin ya yi zanbari.

Fim:Menene ra’ayinkidangane da zargin da ake yicewa ku mata ’yan fim ba kuson aure?

Fatima: To ka san aurenufi na Allah. Duk iya sonkada shi, ba yadda za a yi ka yima kanka wannan aure sailokacin da Allah Ubagiji ya]ibar maka ya yi. Sabodahaka aure ina da ra’ayinsa,amma, wani lokaci... Ka sanko da kana so, ba kai za ka

je ka jawo ]a namiji a jikika ce kana son shi a ]auramaku aure ba. Aure ina sonshi, ina kuma da niyya.Kuma a taimake mu daaddu’a mu samu masu sonmu muke kuma son su, hara ]aura auren.

Fim: Ke ma kina dara’ayin auren ]an wasa]an’uwanki?

Fatima: E, to, a gaskiya bawai ba mu son aurensu bane. Idan ka samu mai son ka

tsakani da Allah za ka iyaauren shi. Ba wai muna}insu ba.

Fim: Daga ciki finafinanda kika yi, wanne ne ya fiburge ki?

Fatima: E, to, a gaskiya kaga kamar Jini [aya yakwanta mani a rai. Domin nayi shi cikin kwanciyarhankali ba wata fargaba, batsangwama. Na fi jinda]inshi.

Fim: A wane fim kika fi

42

Page 44: Mujallar FIM - March 2002

Fim, Maris 2002

ZULAI [alhat sabuwar’yar wasa ce da ta fikowace ’yar wasa

}an}antar jiki a Kaduna, harwasu na ce mata ‘Smally.’ Toamma a fagen shirin fim taba da mamaki a wasufinafinai da aka share matafage ta taka muhimmiyarrawar da ta sa wasu ’yanwasan ke tunanin in ba a yihattara ba, za ta iya shigagaban wa]anda suka da]ecikin sana’ar.

Zulai dai tana da ruwanKanawa. Ainihin babantamutumin Kura ne ta JiharKano. Amma an haife ta aBarnawa, Kaduna, ta yiwayo a unguwar Narayi.Mahaifiyarta kumaBafillatanar Katsina ce.Zulai ta yi makarantarfiramare ta Aliyu Makamada ke Barnawa daga 1988zuwa 1995. Daga nan tawuce sakandare, ta gama acikin 2001.

Mun tambaye ta yaddaaka yi ta shigo harkar fim dasauri haka, maimakon ta cigaba da karatu.

Zulai ta amsa, “E, akwaiwani biki na ranar Hausa daaka yi a ‘Sardauna MemorialCollege,’ Kaduna, wanda’yan makarantar je-ka-ka-dawo da ke Kawo Kadunasuka shirya. To, an gayyaciwani (furodusa), a wajen dayayana Abab, watoAbdurrasheed, furodusanfim ]in Ishara. A nan mukaha]u da su muka saba. Shine sai rannan na jeBadarawa, sai na hange shi(Abdurrasheed), shi ne na cebari in je in gaishe shi.Muna gama gaisawa, sai yatambaye ni, ya ce ina dasha’awar yin fim? Sai na ce

sabsabsabsabsabuwuwuwuwuwar tar tar tar tar taaaaauraruraruraruraruraruwuwuwuwuwar kadunar kadunar kadunar kadunar kadunaaaaa

SHIRIN FIM A KADUNAshan wahala?

Fatima: Ba wanda zan cena wahala a cikinsu.

Fim: Wace shawara za kiba ’yan mata da ke sha’awarshirin fim, amma sun }ishiga saboda gudun surutunmutane?

Fatima: Shawatata ita ce,su manta da surutun mutane,in dai sun sami amincewariyayensu, to su shigo kawai.

Kada su manta: mutum ba aiya mashi, ko me za ka yi saian sa maka ido.

Fim: Ya za ki kwatanta}warewar ku ’yan Kadunada tawarorinku mata ’yanfim na Kano?

Fatima: A gaskiya ’yanmata Kaduna suna }o}ari,wanda ni a ganina, da gasaza a yi na tabbata mu za mu

ci. Wallahi a harkar fim, baabin da ’yan wasan Kano zasu nuna mana, sai dai in ba aba mu dama.

Fim: Akwai wanibambanci da furodusoshi kenunawa tsakaninku da ’yanwasan Kano in an je ]aukarfim?

Fatima: E, a gaskiya an fikarrama su fiye da mu.

Wannan shi ya sa ma su ’yanwasan Kanon sukan ri}a]aga mana kai suna ganinsun fi mu. Amma ba laifinsuba ne, laifin furodusoshin(Kaduna) ne da suke}askantar da kansu sunaneman suna wajen ]an wasa,maimakon ]an wasa yanemi suna wajensu.

Fim: Fatima, mun gode.Fatima: To sai anjima.

mashi, ‘E, a gaskiya ina dasha’awar yi...’ To daga nanne, idan ya ji za a yi fim, shike zuwa ya kai ni wurin.”

A ta}aice, AbdurrasheedMohammed Kankiya nesilar shigarta fim. Zulai ta]auki Abdurrasheed tamkar]an’uwa, tana kiransa‘yaya,’ shi kuma yanakiranta ‘}anwata.’ Wannankusanci nasu ya sa wasusuke tsammanin ko yana

nemanta ne, amma shi da itaduk sun ce sam ba haka abinyake ba.

Fim ]in da ta fara fitowaa cikinsa dai shi ne Adali.Daga shi sai Gagarabadau,wanda mujallar Fim tashirya. A cikin wa]annan,Zulai ba ta fito a wanibabban matsayi ba. Fim ]infarko da ta fito a matsayinjarumar shirin shi ne Illah,wani wanda kamfanin ‘Koli

Trading’ ya yi a Kaduna,wanda kuma bai fito batukuna. Kwanan nan kumasuka gama ]aukar wani fimda su Shu’aibu Idris Liliscosuka zo daga Kano suka yi.Kowa ya ga rawar da ta yi aIllah da wasan su Lilisco, zaitabbatar ba shakka wannanyarinyar ta san abin da takeyi a wasan fim.

Zulai ta nuna haza}a afinafinan da ta yi, wanda yasa mutane suna ganin lallaiidan ta samu dama, to za tahaske fagen fim na Kadunaa bana.

Ban da wasan fim, Zulaita iya rera wa}a, ta yadda inda a ce a Kano take to da tayi zarra a tsakanin zabiyoyinfinafinai.

To yanzu Zulai ta shigowannan kenan, ko kuwa dainan da ]an wani lokaci za tabari?

Zulai ta ce, “A’a, zan soin bari mana. Saboda kagani, ina so in yi aure. Ammaba yanzu ba, yanzumakaranta zan koma.”

To idan ta fara zuwamakarantar, za ta bar shirinfim kenan, ko duka biyun zata ha]a? “Makaranta ba zata iya hana ni yin fim bagaskiya. Saboda ina dara’ayi,” inji ta.

A kan wannan batun, Fimta yi mata tambayoyikamarhaka:

Fim: To shi wanda zai aureki ]in, ]an wasa ne?

43

Page 45: Mujallar FIM - March 2002

Fim, Maris 2002

Zulai: (dariya) A gaskiyani ban san abin da zan ce maba a nan.

Fim: Kina iya gaya mana,ai ba abin kunya ba ne.

Zulai: To, e ... ]an wasane.

SHIRIN FIM A KADUNAFim: A Kano yake ko

Kaduna?Zulai: A Kaduna.Fim: Fitaccen ]an wasa ne

ko sabo?Zulai: Kai, ka cika

bincike, don Allah ka bar nihaka nan!

Shin ko akwai watamatsala da ta ta~a fuskantagame da shirin fim? Zulai tace a gaskiya ba matsalar da

ta ta~a fuskanta. Amma ta ceabin da ya fi yi mata da]i tunda ta shiga harkar fim shi ne,tun da ta fara fim ba ta ta~afa]a da kowa ba. “Wasa dadariya kawai ke ha]a ni dakowa,” inji Zulaihat.

WATA matsala daaka lura masushiryafim na

Kaduna suna da ita ita cershin fitowarim ]insu dawuri. A Kano, dazaranfurodusoshi ya }are ]aukarfim, Allah-Allah yake ya jea ha]a masa hotunan ya kaiwurin tacewa don ya bi layinfitowa. A Kaduna, sai a yifim a }are, amma ka ji shirukamar an shuka dussa. Shinmeye matsalar? Ku]i nebabu ake kame-kame kokuwa?

Muhammad SadisuKudan yana daga cikinfurousoshin Kaduna da sukayi fim, amma ga alama fim]in, mai suna Fauziyyah, yama}ale. Yaro ne mai}aramin jiki, to amma yanamasifar son shirin fim.

Sadisu, wanda wasu kekira ‘Young Producer’saboda }an}antarsa, ya ceshekarunsa ashirin da biyuda haihuwa.

Dalilin da ya sa ya farashirin fim tun yanzu shi ne,“Ni a gaskiya, ina bala’insha’awar yin wasan

kwaikwayo, saboda na farakoyon wasan kwaikwayotun ina firamare, har ta kai

ga muna ]auka mu je gasa awata makaranta. Kamar irinranar Maulidi muna fita a je

‘BA RASHIN KU[I YA TSAYAR DA FIM [INA BA’a yi dirama, ko kuma idanza a yi wani taro na manya,akan gayyace mu. Tun ina}arami ]an shekara gomaana fita da ni a yi wasankwaikwayo, har ta kai ga natafi sakandare a Okene, wato‘Uncle Abdul’Aziz AttahirMemorial College’.

“Da yake can ba Hausawasosai, ina gab da fita, sauranshekara ]aya in gama sai nabaro makaratar na dawoKaduna na shiga G.S.S.Unguwar Sarki. Sai na samuakwai }ungiyar wasankwaikwayo, na shiga, nakuma ri}e ta da hannubibbiyu. Muka ci gabawasan kwaikwayo har darawar }oroso, har muna fitagasa a waje. Har na gamawannan makaranta na shiga‘Polytechnic’ a nan Kaduna.Har zuwa wannan lokaci banbar wasan kwaikwayo ba.”

Fim ta tambayi Sadisu a}ananan shekaru da yake dasu, me ya sa ya zarce yazama furodusa maimakon yafara da zama ]an wasa? Saiya amsa: “Abin da ya sa nayi sha’awar shirya fim nawana kaina shi ne, ina dara’ayin zama furodusamaimakon ]an wasa kawai.”

To ya aka yi ya samuku]in shirya fim,musamman tunda abu nemai tsada? Rance ya yi, kokuwa wani ya ]aukinauyinsa?

Sadisu ya ce, “Wasu dagacikin furodusoshi sunasamun matsalar ku]i, ammani ban ta~a samun matsalarku]i ba tun da na fara fim]ina. Kuma kamar yaddawasu ke tsegumi cewa rashinku]i ne ya tsaida fim ]ina,saboda yanzu fim ]ina yakai misalin wata biyar anashirya shi, ba wai rashinku]i ya tsayar da shi ba.Abin da ya tsaida aikin shine, muna so mu samu fimmafi inganci, shi ya sa akaSadisu (a tsakiya) tare da su Sani Musa Danja lokacin daukar shirin Fauziyyah

Muhammad Sadisu Kudan

44

Page 46: Mujallar FIM - March 2002

Fim, Maris 2002

]auki wannantsawon lokaci fim]in bai fito ba.

“Wasu suna gania gaggautakammala shiri fimshi ne gwaninta.Wai ka yi sauri kagama fim bagwaninta ba ne. Niina tsammanincewa nan dashekara biyar masuzuwa fim ]ina yananan daram yaddayake ba zai canzaba, kuma zai iyatafiya da kowanezamani. Kuma koyanzu na saki fim]ina na tabbata dawuya a samu fim]in da ya yiingancin aiki da fim]ina ya samu.”

A kan batunsana’a Sadisu ya ceshi dai ]anmakaranta ne,amma yana saidakayan gini.

Ban damatsayinsa nafurodusa, Sadisuyakan shiga fim a yiwasa da shi saboda,a cewarsa, da masaboda sha’awaryin wasan ya sa shihar ya zamafurodusa. Ya fito afinafinai da sukaha]a da wani na‘ H a s h i m a w aMovies’ a nanKaduna mai sunaDaula, da kumawani da ’yanUnguwar Sarkisuka shirya, dawasu biyu. Gakuma uwa-ubawanda yakeshiryawa.

Fim ta tambayeshi ko zuwa yausheyake sa ran fim]insa zai fito?Sadisu ya ce, “Aina gaya maka cewani fim ]ina bin shinike a hankali ne.Saboda haka yanzuba zan iya gayamaka cewa galokacin da fim ]inazai fita ba.”

To, muna jira.

SHIRIN FIM A KADUNA

ASHE dai gaskiyar Bahausheda yake cewa, “Abin da yaci Doma, ba ya barin Awai.”

Kamar yadda ’yan wasan Kaduna kekokawa dangane da mayar da susaniyar ware da furodusoshinKaduna suka yi, su ma daraktocinna Kaduna abin ya shafe su. Hakanyana ci masu tuwo a }warya, domina cewar wasu daga cikinsu, har takai ga wasu takwarorinsu na Kanosuna yi masu shagu~e.

[aya daga cikin matasan ’yan fimna Kaduna da ake ganin zai ba damamaki a bana idan ya samu fili shine Al-Amin Ciroma, wanda yake~ngren aikin ba da umarni a fim.

Shi dai Al-Amin, a da an san shine a matsayin ]an wasa, amma saiya riki]e ya zama darakta. Ko yayaabin ya faru?

“Ai ko na ji da]in wannantambaya, domin ta zo daidai lokacinda ake bu}atarta,” inji shi. “Da farkodai ban karanta Theartre Art (ilimindirama) ba, abin da na karanta shine komfuta. Da ma can ina matu}arsha’awar finafinai, ana cikin haka saina zo Kaduna har na ha]u da wasufurodusoshi, suka kuma kar~e ni,har aka fara shirin fim da ni. Akwaiwani fim mai suna Aure Ko Boko?,shi ne na farko da aka fara yi da ni.To saboda tsananin ra’ayin da nikeda shi a kan shirin fim, sai kawai nayi tunanin cewa komai da gwaji akefarawa. Saboda wannan ra’ayi nawatun farko, so nike in ga cewa na shigacikin wannan harkar tsundum, sai nafara kusantar wasu daraktocin,kamar su Francis Mai}arfi naK.S.T.V. da kuma wani daraktaLivinus Oteh, har ya zuwa kamar suMalam Saminu, da dai sauransu.

“Da na tashi gwada basirata sai nafara da wani fim mai suna Sara DaSassa}a. Koda yake dai ba ni ka]aina yi aikin ba, amma na ba damuhimmiyar gudummuwa. Daganan ne na mi}e na fara ba da

ummarni gada-gadan”.Al-Amin ya ba da umarni

a finafinai da dama ya zuwayanzu, har ma ya kasa ba muadadinsu. Sai mun lura cewabaki ]ayansu finafinai ne na}anana ko sababbinfurodusoshi. Shi ma Al-Amin yana fama da matsalar]auko daraktocin Kano dafurodusoshin Kaduna ke yi,inda za ka ga an maida shimatimakin darakta kawai.

Ko me ya sa manyanfurodusoshin Kaduna ba suba shi aikin finafinansu?

A ganin Al-amin Ciroma,“A gaskiya zan iya cewarashin kishi ne ko ganin}yashi. Domin takwarorinsuna Kano ba haka suke ba.Irinmu-irinmu ne sukatallafa mawa har suka kaimatsayin da furodusoshinamu suke gadara da su.”

Su furodusoshin Kadunasun ]auka cewa daraktocinda ke Kano sun fi na Kaduna}warewa. Al-Amin baiyarda da haka ba. “Batun}warewa,” inji shi, “ba zaniya cewa ga wa]anda suka

DARAKTA MAI |ULLOWA!

fi wasu ba, amma a yanzuhaka idan ka kalli aikinKaduna da na Kano za a gabambanci, domin ka san muda ilimi muke aiki ba kame-kame ba.”

To ko wannan na nufinyana ganin da za a sa gasarba da umarni zai iya karawada kowane darakta dagaKano? Al-Amin Ciroma yaamsa: “A shirye nike,wallahi ina ce masu kulle!Zan iya karawa da kowa.”

To, ga fili nan ga kumadoki.

45

Page 47: Mujallar FIM - March 2002

Fim, Maris 2002

SHIRIN FIM A KADUNA

KAMAR yadda dayawa daga cikin ’yanwasan Kaduna ke

kokawa da cewafurodusoshin Kaduna kehana su damar baje kolinsua cikin finafinai, saboda baba su saka su a wani matsayida ya taka kara ya karya acikin finafinai, shi ma Isma’ilIsyaku Koli hakan ya ]auka.

Isma’il dai sabon ]an wasane wanda ya ba da mamaki}warai da gaske, ganin iringagarumar rawar da ya takaa matsayinsa na jaruminfinafinai biyu na Kaduna -Juriya (wanda ya fito) dakuma Illah (wanda bai fito batukuna). Ha}i}a duk wandaya kalli Juriya, zai yitsammanin da Isma’il ne akabu]e harkar shirin fim tunfarko.

A da, wa]anda suka sanwannan matashi sun san shine a kan sana’ar sayar dakaset kawai, amma yau an

46

wayi gari ya shiga jerinjaruman fim. Yayin da yakebayyana mana dalili, ya ce,“Ka san komai ba yadda kaiya, ko ba haka ba? Kawaikana cikin harka za ka ga katashi ka koma wata. To ni daikawai sha’awa da son abin,da kuma gyaran rayuwaral’umma, shi ya sa kawai natsunduma a cikin wannanabin.” Ya }ara da cewa kafinya shiga sai da ya yi shawarada wasu mutane sosaisaboda gane makamar aikin.Sun ha]a da Ali Nuhu,Hamisu Iyan-Tama, daAminu A. Shariff (Momo).

Isma’il dai ]an shekara 21ne, kuma haifaffen garinKaduna. Ya yi karatunfiramare a UnguwarMu’azu, Kaduna, nasakandare kuma a KwalejinHoron Malamai ta Kaduna,inda ya shekara uku kafin yakoma makarantar kimiyyada ke Birnin Gwari, inda ya

SHIN KO ISMA’IL ISYAKU

ZAI RIKE KAMBIN WASA A BANA?

shekara ]aya, sa’annan yakoma sakandaren‘Command’ ta Kaduna yakammala karatunsa nasakandare.

Asalin Isma’il, Bakatsinene, Bafillace, ta ~angarenuba. Uwarsa ’yar Gombe ce.Ya fara fim ne lokacin aka]an ma}ala shi ya fito cikinshirin Wasila. Daga nan yafito a wasu da suka ha]a da{auna, Juriya, Illah, Bazata,da Taqidi. A cikin wa]annanfinafinan ya fi son {auna,inda ya fito a matsayinabokin Momo. Da akatambaye shi dalili sai ya ce,“Kawai haka nan, sabodalabarin ya burge ni, sannankuma da yadda aka shiryafim ]in.”

Wasannin da Isma’il ya yisun sa yanzu a Kaduna anaganin zai zama babbanjarumin garin a bana,musamman idan ya ci gabada fitowa a finafinan da akeshiryawa a Kaduna da Kano.Ga alama, shi kansa yafahimci haka, domin damuka tamabaye shi ya fa]iwani abu a kan kwatanta

}warewarsa da tatakwarorinsa na Kano, sai yace a gaskiya }warewarsu zata iya zuwa ]aya, wato baiganin sun fi shi. “Kuma kasan Allah yakan ba kowalokacinshi. Saboda haka inaganin mu ma yanzulokacinmu ne aka ba mu,”inji shi.

Isma’il dai lokacinsa yazo. Akwai finafinai da damaa gabansa, musamman matunda kamfaninsu ‘KoliTrading Company’ ma sunfara shirya manyan finafinainasu na kansu inda zai ri}afitowa. To amma duk dahaka dole ne ya san yaddazai iya hul]a da jama’a,musamman abokansana’arsa a Kaduna da Kano;ya san yadda zai ja ra’ayinfurodusoshi da daraktoci susaka shi a fim, da yadda zaiyi tarayya da ’yan fim mazada mata, da kuma masukallo. Idan har ya na}alcisiyasar yadda ake hul]a aIndustry, to ba da jimawa baza ka ji sunansa ya fita,sa’annan ya ci karensa babubabbaka.

Isma’il dai lokacinsa ya zo. Akwai finafinaida dama a gabansa, musamman ma tunda

kamfaninsu ‘Koli Trading Company’ ma sunfara shirya manyan finafinai nasu na kansuinda zai ri}a fitowa. To amma duk da haka

dole ne ya san yadda zai iya hul]a dajama’a, musamman abokan sana’arsa a

Kaduna da Kano...

Isma’il Isyaku Koli

Page 48: Mujallar FIM - March 2002

Fim, Maris 2002

SHIRIN FIM A KADUNA

47

A KANO, dillalankaset, a cikin tarin’yan kasuwa, tuni

suka gano sirrin cin moriyarharkar fim. Don haka sukashiga cikin harkar dumu-dumu ana damawa da su. AKaduna ma, takwarorinsusun fara gano bakin zaren,domin su ma sun shigasana’ar shirya fim, watosuna cin tudu biyu kenan: susayar wa furodusoshi fimkuma su ma su shirya fim.

Alhaji Kabir Karama, maikamfanin kaset na ‘Karama’da ke Kaduna, yana ]ayadaga cikin irin wa]annan’yan kasuwar, domin kuwaya shirya fim mai sunaAbdulmalik, wanda tuni yafito. Sai dai bambancinKabir Karama da saurandillalai shi ne shi da ya tashishirya nasa fim ]in, bairungumi ’yan’uwansaHausawa ba sai ya kwasoInyamirai ya sakar masuragamar aikin. Mai kula dashirya fim ]in da mai ]aukarhotunan bidiyon fim ]in dadaraktan duk Ibo ne. PrinceOscar Baker Anuruo, wandaya shirya finafinan[an’adam Butulu, Jamila,da Macijiya, shi ya jagorancishirya fim ]in.

Akwai mutanen da suka yi}orafin hana su aikin daKarama ya yi, ganin cewafim ]in Hausa ne kuma suHausawa ne. Suna cewa donme ya ]auko su Oscar sukayi aikin, bayan ga su?

To, Karama ya amsawannan tambayar a watahira da ya yi da mujallar Fimkwanan baya, ya ce, “Abinda ya ba ni sha’awa da suOscar shi ne fim ]in da sukayi na [an’adam Butulu daJamila, musamman yaddasuke tsayawa su yi directingfim, da inganci na fim ]in.Sai na ga ya kamata injarraba shi in ga yaya yake,dangane da bambanci

tsakaninsu da namu.”Sakamakon haka sai

Karama ya tuntu~i Oscar dakansa, ya ce ya zo su ha]utare su yi “wannan aikin donmu samu ci-gaba.”

Wata matsala da akansamu idan za a yi fim da ’yanwasan da ba su jin yaren dashi daraktan ke magana dashi ita ce rashin fahimtarjuna. A shirin Abdulmalik,inji Karama, ba a fuskanciwannan matsalar ba. “Dukartists ]in da muka kira sunajin Turanci, suna iya karantaduk abin da za a ce masu,”inji shi. Ya }ara da cewa,“Kuma shi ma darakta ]inya ji da]in irin yadda yazamana tsakaninshi da ’yanwasan bai samu matsala ba.Saboda shi Turanci yake ji,su ma suna ji; duk irinkalmar da zai nuna masu daTuranci, za su fahimta kumasu juya ta da Hausa, kumatsarin ya tafi daidai da abinda ake so. Alhamdu lillahi,mun samu haka.”

Shin kwangila ya baInyamiran suka shirya masafim ]in? A’a, inji shi, ku]isuka ha]a suka yi fim ]in.

A cewar Alhaji KabiruKarama, shi da abokanhul]ar tasa sun }iyasta cewasun kashe kimanin nairamiliyan ]aya da dubu ]aribiyu (N1.2m) wurin shiryafim ]in, komai da komai.

An ]auki shirinAbdulmalik da irinkyamarar nan ce maiinganci, wato Betacam, irinwacce ’yan Kudu sukeamfani da ita suna yin

finafinansu. To, yaya zaikwatanta nagartar fim ]in dasauran finafinan da yakesayarwa? Karama ya amsa,“Gaskiya ba zan iya cewakomai ba. Mai kallo shi nezai iya ba da labarin abin daya gani.”

To, mai kallo, gare ka!Karama ya gaya wa

wakilinmu cewa da }yar nezai iya ]auko wani mutumya shirya masa fim in baOscar ba. Dalilinsa: “Tafiyar

Ina hul]a da }abilu a bisatsarin addinina

da muke yi, na fahimce shi,ya fahimce ni.”

A sane yake cewa wasu zasu iya yin tsegumi a kanwannan hul]a tasa daInyamirai, tunda a wannanharkar akwai }abilanci.

Karama bai damu ba. Gayadda yake kallon abin:“Kullum in mutum zai yiabu, sai ya jarraba, yakwatanta shi da yaddaMusulunci ya ce. Musulunciya yarda ka yi kasuwanci dakowa, matu}ar babu zaluncia ciki. To Oscar mun yiwannan abu da shi, baizalunce ni ba, ban zalunceshi ba. Saboda haka maganarBahaushe ko ba Bahausheba, ni dai abin da na sani shine mun yi yarjejeniya daOscar kamar yadda Shari’ata ce.”

Alh. Kabiru Karama

– Karama

“Kullum in mutum zai yi abu, sai ya jarraba, yakwatanta shi da yadda Musulunci ya ce. Musulunciya yarda ka yi kasuwanci da kowa, matu}ar babu

zalunci a ciki. To Oscar mun yi wannan abu da shi,bai zalunce ni ba, ban zalunce shi ba. Saboda haka

maganar Bahaushe ko ba Bahaushe ba, ni dai abin dana sani shi ne mun yi yarjejeniya da Oscar kamar

yadda Shari’a ta ce.”

Page 49: Mujallar FIM - March 2002

Fim, Maris 2002

http://groups.yahoo.com/group/

Hausa Home Video Bulletin Board at Yahoo!GroupsCreated: Friday August 31 st , 2001email: [email protected] page: http://groups.yahoo.com/group/Finafinan_HausaGroup Owner/Moderator: Professor Abdalla Uba Adamu([email protected])Group Moderator: Ibrahim Sheme ([email protected])To join: http://groups.yahoo.com/group/Finafinan_Hausa/join

WANNAN wani zaure ne da aka }ir}ira a dandalinsadarwa na zamani, wato intanet. An gina zaurenne a kan tsarin ‘Groups’ na babbar masana’antar

sadarwa ta intanet da ke Amerika ]in nan mai suna Yahoo!Shi tsarin “Groups’ yakan bai wa gungun mutane masura’ayi daban-daban damar su tattauna a kan wani al’marida ya tara su a zauren. A wannan zauren namu, mutanesuna tattaunawa ne musamman a kan finafinan bidiyo naHausa, wa]anda ake yayinsu yanzu. Suna da adireshinzauren su ne: [email protected] gudanar da shi su ne Furofesa Abdalla Uba Adamuna Jami’r Bayero, Kano, da Ibrahim Sheme na mujalarFim. Duk mutumin da ya mallaki adireshin i-mel zai iyashigowa zauren ya shiga cikin tattaunawar da ake yi a ciki.To, alhamdu lillahi yanzu wannan zaure dai ya bun}asa,domin akwai ]imbin mutane (wasu a Nijeriya, wasu aSaudiyya, wasu a Amerika, wasu a Turai, wasu a Afrika taKudu), wa]anda membobin zauren ne.

Mujallar Fim tana kwafo dukkan muhawarorin da ake

yi a zauren, don masu karatunta su ga yadda mutane sukefurta albarkacin bakinsu a kan harkar fim. Wannan zai ba’yan fim da sauran masu karatu wa]anda ba su shigazauren ba a da damar sanin me ake cewa a cikinsa.

Za ku lura cewa yawancin maganganun da aka yi daTuranci ne ake yin su. To, wannan za~i ne na masurubutun, kamar yadda aka ta~a yin muhawara a kai. Idankana so ka yi magana da Hausa, shikenan. Mun yankeshawarar bar wa kowa abinsa kamar yadda ya rubuta (batare da gyarawa ba ko canza masa wani abu cikinbayaninsa) domin a ba kowa ’yancin ya fa]i albarkacinbakinsa, wanda wannan ’yancin yana daga cikin manyanginshi}an ita kanta hanyar intanet. Don haka idan ka gakuskuren nahawu a rubutun wani, ba laifinmu ba ne.

Wanda ke so ya shiga zauren ya zama memba, kawaiya duba wannan adireshin ya shiga, wato:http://groups.yahoo.com/group/Finafinan_Hausa/join

A sha karatu lafiya!

13From: [email protected]: Sat Sep 8, 2001 4:31amSubject: Iam happy

HI every one, i think this is the right time for the hausa’s tocontribute to their culture through the net.Also we shouldstart to write in hausa.

*14From: Dayyabu Usman <[email protected]>Date: Sun Sep 9, 2001 10:21amSubject: Messages

Group Moderator, I recently joined the above named groupon Yahoo but I cannot access the messages sent online.Can you please advise me on what to do so that I cancontribute my own quota towards the goal of this e-group.Reply ASAP.

Dayyabs*

15From: Dayyabu Usman <[email protected]>Date: Sun Sep 9, 2001 10:32amSubject: Disregard Messages

Hello everybody, Reference to the mail I sent with subject

Messages, at about 6:20 pm on Sunday 9th September 2001,I am hereby notifying brothers and friends to disregard thecontent of the mail. Well, as all of know we learn everyday, Ihappened to be new in using a Yahoo e-group but Idiscovered how to use it now. In the future if I ‘ve any problemI will not hesitate to ask my brothers to avail me.

In my opinion this group should not only serve as a forumfor films issue only but as an electronic tool or school for themembers.

Regards, Dayyabu Usman*

16From: Dr. Abdalla Uba Adamu <[email protected]>Date: Sun Sep 9, 2001 0:52amSubject: Re: Disregard Messages

DayyabsThanks for the post! Don’t worry about finding your way

around the egroups homepage. We all started like that! Iadmit it can be abit confusing sometimes, but if you do getgood connection, try to spend at least 10 mins exploring thehomepage, and then all things will fall in place. Remember,you can also post files (e.g. papers or articles you have writtenabout Hausa home videos), or photos, e.g. if you have aphoto of a Hausa megastar like Ali Nuhu, and he doesn’t

mind his pic appearing here, you can post it. When weget enough members (e.g. lots!!) we will run our ownKanywood “Oscars” through the Polls option at the left sothat people can vote the best Hausa film they have seen.This might guide our colleagues, friends and researchersoutside the country as to what is hot and what is cold inSabon Titi Hollywood Boulevard, Kano, Nigeria!

I will be posting more home video movie posters tobrighten up your desktop!

Salaam!Abdalla Uba Adamu

48

yahoogroups logo

Page 50: Mujallar FIM - March 2002

Fim, Maris 2002

BUK, Kano, Nigeria*17From: Dr. Abdalla Uba Adamu <[email protected]>Date: Mon Sep 10, 2001 2:41amSubject: Re: Iam happyYour point is well taken. But the idea behind an internet-

based club like this one is to attract other people who maynot necessarily be conversant with the Hausa language. Weset up this forum to propagate our culture, especially to thoseoutside Northern Nigeria. My view is that any Hausa savvyenough to join this club would definitely understand themessages here.

But who do others think? Should we be all Hausa-onlymedium, or can people say it the way they want?!

Feedback please. Get involved. Recommend this site toothers. Let’s make Mujadala bigger than The Gladiator!!!

Regards to allAbdalla*

18From: Fatima Abubakar <[email protected]>Date: Mon Sep 10, 2001 4:42pmSubject: Re-I AM HAPPY

Assalamu Alaikum,If kdantata feels we should start writingin Hausa language, why not? We can write in both languagesas the occasion demands,some things are better expressedin Hausa while some are more meaningful in english.I amsure Dr.Abdallah will agree with me as he is fond of mixingthe two languages to put accross his messages.MeanwhileI watched Uzuri last night and I supposed it was meant to bea tragedy but to my mind it turned out to be a comedy,whatwith Mandawari folding his babbanriga to beat a cripple andHafsatu Sharada shouting “maye” in the Police station as ifthe Police have anything to do with cases of maita.Kudiri isan Indian film no doubt as Hausa culture does not haveanything like a whole family going to visit their prospectivebride’s family only for the kids to go out and sing and danceto their heart’s desire.What do you feel all of you out there?But Saima Moh’d.deserves an award for her role in thefilm.Waiting for your responses.

Ma’assalam,Fati.*

19From: Dr. Abdalla Uba Adamu <[email protected]>Date: Mon Sep 10, 2001 10:19pmSubject: Indianization of Hausa Home Videos

Salaam everyoneI don’t want to be too “cliqued” by saying I am happy

everyone is happy! It is good that at least someone hasreacted to something. You may find this ironic, but the onlyHausa home videos I have actually sat down and watchedare two: Laifi Tudu Ne, and Mukhtar 2. The reason forwatching the first was because one of the ExecutiveProducers is a friend and he gave it to me free! The reasonfor watching the second is also because it was given to mefree by the Director, and also it was shot in my house! Whatis even more ironic is that I actively purchase two or so ofthese videos every week for my family who are avid fans(my three year old can mime to all the dance routines inMujadala 2!).

So how come a non-fan of these movies sets up a site forthem? Simple, they are cultural expression and where cultureis concerned, I am in as deeply as I can get involved. So Ihave not watched Uzuri, but I am sure one of the membersof family must have seen it either when I bought it (can’teven remember the titles!) or through their underground video

swap network. This leads me to an issue raised by HajiyaFati and that is the increasing Indianization of Hausa films.While the logic of using song and dance routine to makevideos marketable is understandable from businessperspective, yet from the cultural perspective sometimes suchactivities are ridiculous. For instance, I find the high-pitchedvoices of our singers, especially the female ones, ratherembarassing. Also the Indian gestures of hand, face andbody employed by our actors (from the snippets that I seewhen the family is watching) are of course uncharacteristicof Hausa body language. Admitted there has always been asong and dance in the dandali playtimes of Hausa (gadar‘yan mata, etc), but our modern video producers haveelavated the process to an Indian platform. I suppose that iswhy I liked Laifi Tudu Ne — there wasn’t a single song in it(the characters, however, danced to a tune played from atape).

So, what do others also think? More Indian or less Indian?More traditional (e.g. do people prefer Dan Ibro’s kind of playsto Ibrahim Mandawari’s.

Write on!!!Abdalla*

20From: [email protected]: Mon Sep 10, 2001 10:28pmSubject: New file uploaded to Finafinan_Hausa

Hello,This email message is a notification to let you know that a

file has been uploaded to the Files area of theFinafinan_Hausa group.

File : /Bidio - Akasi.jpgUploaded by : [email protected] : Bidiyo - AkasiYou can access this file at the URLhttp://groups.yahoo.com/group/Finafinan_Hausa/files/

Bidio%20-%20Akasi.jpgRegards,auadamu@y...*

21From: [email protected]: Mon Sep 10, 2001 10:30pmSubject: New file uploaded to Finafinan_Hausa

Hello,This email message is a notification to let you know that a

file has been uploaded to the Files area of theFinafinan_Hausa group.

File : /Bidiyo - Tallafi.jpgUploaded by : [email protected] : Bidiyo - TallafiYou can access this file at the URLhttp://groups.yahoo.com/group/Finafinan_Hausa/files/

Bidioy%20-%20Tallafi.jpgRegards,auadamu@y...*

22From: [email protected]: Mon Sep 10, 2001 10:32pmSubject: New file uploaded to Finafinan_Hausa

Hello,This email message is a notification to let you know thata file has been uploaded to the Files area of the

Finafinan_Hausa group.File : /Bidiyo - Badali.jpgUploaded by : auadamu@y...

49

Page 51: Mujallar FIM - March 2002

Fim, Maris 2002

Description : Bidiyo - BadaliYou can access this file at the URLhttp://groups.yahoo.com/group/Finafinan_Hausa/files/

Bidiyo%20-%20Badali.jpgRegards,auadamu@y...*

23From: [email protected]: Mon Sep 10, 2001 10:34pmSubject: New file uploaded to Finafinan_Hausa

Hello,This email message is a notification to let you know that a

file has been uploaded to the Files area of theFinafinan_Hausa group.

File : /Bidiyo - Da Wa Zan Kuka.jpgUploaded by : [email protected] : Bidiyo - Da Wa...You can access this file at the URLhttp://groups.yahoo.com/group/Finafinan_Hausa/files/

Bidiyo%20-%20Da%20Wa%20Zan%20Kuka.jpgRegards,auadamu@y...*

24From: [email protected]: Mon Sep 10, 2001 10:36pmSubject: New file uploaded to Finafinan_Hausa

Hello,This email message is a notification to let you know that a

file has been uploaded to the Files area of theFinafinan_Hausa group.

File : /Bidiyo - Dan Halak 2.jpgUploaded by : [email protected] : Bidiyo - Dan HalakYou can access this file at the URLhttp://groups.yahoo.com/group/Finafinan_Hausa/files/

Bidiyo%20-%20Dan%20Halak%202.jpgRegards,auadamu@y...*25From: jamilu haris <[email protected]>Date: Wed Sep 12, 2001 4:00pmSubject: Re: Re-I AM HAPPYHI every one,I Think is good to write in both hausa and english.bye*26From: Dr. Abdalla Uba Adamu <[email protected]>Date: Thu Sep 13, 2001 3:14amSubject: Re: Re-I AM HAPPYTo Mallam, ai sai ka fara daga yanzu. Allah Ya ba mu sa’a,

Amin!*

27From: Tracy Johnston <[email protected]>Date: Fri Sep 14, 2001 8:56amSubject: Re: Re-I AM HAPPY

Abdalla - THANKS! IT’S GREAT TO HEAR FROM YOU! Ihave spent half the day reading all your mail. Your resumealone took 2 1/2 hours! And the stuff on Kanoonline. VERYinteresting. Doesn’t help me with my novel, but I am glued tomy screen I’ll get back to you when I’ve checked outeverything. Couldn’t find out how to read what’s going on inthe Hausa news group. Do I have to post a message? Are

there archives?More later,Tracy*28From: [email protected]: Thu Sep 13, 2001 10:17pmSubject: Finafinai Da Ta’addanci A AmurkaYan Uwa,Game da abin da ya faru ranar litinin a kasar Amurka,Ina

fatar abin bai shafi ko daya daga cikinmu ba. Ina fatar kumabai shafi kowa da muka sani ba. Allah ya tsare gaba kumaya kawar da mugayen kaddarori.

Bayan haka, tun da wannan wurin haduwar masu harkada kuma sha’awar finafinai ne, ina gayyatarku ku yi kallonwasu finafinai biyu wadanda suka bada karfi ga irin wadannanharkokin ta’addanci a cikin kasar Amurka. Na farko shinewani fim mai suna “Arlington Street” (Jeff Bridges da TimRobbins). A wanan fim dai, wani shahararren dan ta’addane (Tim Robbins) farin ba’amurke wanda ke makwabtaka dawani mutum wanda ya rasa matarshi ma’aikaciyar FBI a wanikaron ta’addanci (Jeff Bridges). A karshe dai wannan danta’adda ya yi makarkashiya har ya tura wannan makwabcinshi(ba a cikin sanin makwabcin ba) ya rugurguza hedikwatarFBI a Washington da wasu bamabamai masu karfin gaske.

Na biyu shine wani fim mai suna “The Siege” (DenzelWashington da Bruce Willis), inda shi Denzel washingtonwani jami’in FBI ne mai jagorar kawar da ta’addanci a cikinkasar Amurka. Sai wasu mutanen larabawa suka tayar dahankalin kasar Amurka a cikin garin New York har aka kirakwamandan rundunar sojojin Amurka (Bruce Willis) ya zo yakama su ya rugurguza su. Amma shi wannan jami’in FBIhankalin shi ya rabu biyu domin, ya kamata a ce shi maikare rayuwar Yan Amurka da mazauna a Amurka ne ba maihalaka su ba. Wannan rabon hankali ya kawo rashin jituwatsakanin shi da wannan kwamandan sojan.

Idan kun same su kun kalla, ku gaya min naku karin bayani.Mohammadu Bello Salihu,Shugaban Wayar internet ta HausaNet.com*29From: Yusuf Adamu <[email protected]>Date: Thu Sep 13, 2001 11:55pmSubject: Re: Finafinai Da Ta’addanci A AmurkaMuhammadu Bello,Mun gode da wannan bayani. Muna nan lafiya, muna fatan

kuma Allah Ya kara tsare mu amin.Yusuf Adamu*30From: Dr. Abdalla Uba Adamu <[email protected]>Date: Sat Sep 15, 2001 2:10amSubject: Re: Finafinai Da Ta’addanci A AmurkaSalaamAkwai fim na uku wanda watakila ka manta da shi. Wannan

kuwa shi ne Executive Decision na Kurt Russel da kumaSteven Seigal, a inda aka yi hasashen wani jirgin sama yataho zuwa Washinton cike da bam. Aikin Kurt Russel ne yashigar da ‘yan tsaro cikin jirgin, sannan kuma a hana bamdin daga tashi.

Abdalla*31From: Amina Ibrahim <[email protected]>Date: Tue Sep 18, 2001 1:19amSubject: Lets not sell our culturesAssalamu alaikum everyone,I was very happy when I went to check my mail and found

50

Page 52: Mujallar FIM - March 2002

Fim, Maris 2002

your contributions. I am very proud of the way things aregoing on. I am not really good at watching films, until lately,I started with comedy, the best sellers, Nigerian films andfinally Hausa films. It is not that I have stopped watching allthese films I have mention but now I concentrate on Hausafilms fully. Our only problem is the way the films are beingproduced. Most films are produced only to make money, nogood storyline, poor costumes, bad location and repeatingof actors because of selfish interest, if we can eliminate quackproducers in directors from the Hausa film industry, I think itwill reduce quack films which have no meaning.

Fatima Abubakar, I like your write up. Most of our films arecopied from Indian films. Hausa and Indians have differentcultures; we should not sell our cultures and buy the Indianculture, like the Indians did. You know they sold their cultureand became Americans overnight. The dancing and singingin our films is something I have really thought of, we cantreally stop it now because it has become a virus in our wom-en’s system. Take for example FALLASA which had a verygood message, but when I researched, only few copies weresold because there was only sound track, no dancing norsinging. If the viewers, that is those watching the film, want itlike that then let’s allow it. I am not a good writer or should Isay a good composer, so bear with me. Ma’assalam.

Amina Ibrahim Ozoza*32From: Dr. Abdalla Uba Adamu <[email protected]>Date: Tue Sep 18, 2001 5:52amSubject: Re: Let’s not sell our culturesSalaam to allI thought these dialogs will be in Hausa!! But whatever, do

what makes you feel comfortable because some thoughtsare probably easier to express in English for some people.

Amina, don’t judge the producers and directors of Hausahome video too harshly. Remember, they are in it to makemoney, not to promote culture. As you pointed out, films thatdon’t have song and dance routines don’t sell well; in Kanothe audience walked out of LAIFI TUDU NE because theprincipal actors were killed BEFORE the end of the film! Andyet I consider it one of the most well-crafted Hausa homevideos, and if I am entering a Hausa film for an internationalcompetition, I would certainly include it (with KOGIN BAGAJAwhose song and dance were based on rural settings, veryrealistic). No producer worth his naira would take on a moviesimply because he wants to be artistic. Again you must alsorecognize that some of the home video producers learn, asit were, on the trade. Although I don’t believe you have to betrained for something before you can become an expert in it,nevertheless some amount of orientation is needed if a per-son is to move away from a plain garage-producer to a world-class producer.

Look at it this way: the producers are making money. Theyare happy. The audience loves their movies, they are buyingthem. That is what capitalism is all about — satisfying con-sumers. At the moment the audience is saying they wantsong and dance, and that is what they are getting from theproducers. Like you, I look forward to the day when I will seea movie that is really artistic, reflecting Hausa culture andgiving value for money. For an analysis of how the worldsees the Hausa efforts in home video production, follow thefollowing links:

h t t p : / / w w w . s h o b a k . o r g / s a m a r / a r c h i v e /bollywoodnigeria.html

h t tp : / /www.barnard .co lumbia .edu/anthro /h tml /bios_brian.html

So what do people think: acculturation or cultural colora-tion?

Salaam to allAbdalla*33From: Hadiza Ibrahim <[email protected]>Date: Wed Sep 19, 2001 3:47amSubject: Re: Let’s not sell our cultureSalam Everyone out there!!!Dr. Abdalla, don’t you think Amina is entitled to her opin-

ion? I do not agree with the idea of filmmakers doing it formaking money, I thought even though we are in a corruptsociety, there some good people around us. You don’t dothings just because you want to get away with your money. Iknow it’s their fortune they put into making these films, butit’s too obvious that the whole thing is based on makingmoney. Down here people would have love to be buyingsubtitled Hausa films if only no songs and dance, naturallywe the Hausas so much like Indians from the look of thingsbut that is not a reason for us to leave our culture for theirs.

You see giving people what they want is okay, but not eve-rybody wants dance and songs in films. I agree with you themajority matters, but what about cases where producers re-peat films, or just make any film to make money and oneend up watching just nothing? I watch Hausa films eventhough I do that only when am back home in Kaduna but yetI get along, not when half of the films carry advert, danceand songs. Nevertheless, our producers are trying but thedirectors should please put more effort, make these thingslook real, so that our money is justified to what we watch.

I can understand Amina’s stand, she is just scared of ourpeople don’t go “gaga” the way the Indians are now.

CheersHadiza Ibrahim.*34From: Dr. Abdalla Uba Adamu <[email protected]>Date: Wed Sep 19, 2001 5:42amSubject: Re: Re: Let’s not sell our cultureSalaam To all (this is a multiple-response posting, so it is

not only restricted to the third poster in the thread only).Of course I am not disputing Hadiza’s views and it is healthy

that she, like everyone else, can actually post what is in theirminds. After all, this is the reason why I set up this forum —for people to interact and exchange views, no matter howdivergent.

The point of my posting is a reality check. There are quitea few people who don’t like the song and dance routines ofHausa movies. I personally find them ridiculous andembarassing. However, there are equally many people, in-deed the VAST majority, who watch the Hausa movies pre-cisely BECAUSE of the song and dance routines. I onlypointed out that producers and directors are reacting to thedictates of market forces. Hadiza herself pointed out a moviethat did not sell well because it lacks the necessary songand dance routines. I agree not all the Hausa filmakers arein it for making tons of money.

Regretfully, however, MOST of them, and they constitutethe majority, are in it to make money, not to make artisticcommentaries on Hausa society. However, we can changethis. Right now the Hausa home video industry has rede-fined the concept of entertainment in Northern Nigeria. Fiveyears ago the heroes of youth were Indians. Now it is AliNuhu, Fati Mohammed, Maijidda, Ciroki, Dan Ibro and oth-ers. All Black, all Africans and all Nigerians. For the BlackPride thing, this is only excellent.

-------------------------------------------------------------------Za mu ci gaba da kawo maku wadannan hirarrakin a Fim

ta watan gobe. Ku biyo mu. Edita

51

Page 53: Mujallar FIM - March 2002

Fim, Maris 2002

Ayyiriri!! ’yan fim sun yi selula!WAI wai wai!!!” inji Ciroki.

Yanzu ’yan fim sun shigacikin wata sabuwar rayuwa

sakamakon fara amfani da hanyar isarda sa}o ta GSM, musamman a Kanoda Kaduna. Za ka yi dariya har cikinkaya yi ciwo idan ka tsaya gefe ]aya kaga yadda wasu ’yan fim maza da matake }arya da ba da fa]i da tarhon aljihuna GSM. Na karanta a jaridu cewagwamnatin }asar Finland har doka takafa kan kamfanoni masu }era tarhomobayil, ba don komai ba kuwa sabodasun yi yawa a }asar. Kai ko a }asarAfrika ta Kudu a birane irin suJohannesburg kowane direban tasi saiya mallaki irin wannan tarhon sannanzai yi tu}i. Ko a }asar Ghana, waniwakilin wata jarida da ake bugawa aAbuja ce min ya yi ya ga ’yan aca~a dayawa da ita.

Amma mu a nan da yake yanzu tashigo, wasu masu ita su gani suke kamarbabu ba}auye sai wanda ba shi da ita.Ko lokacin da tarhon mobayil ya farafitowa a duniya, a London ba wanijinsin mutane da suka fi yin ‘barazana’da mobayil irin ’yan Nijeriya. [anArewa a Landan kenan! Mu dawo fagenshirin fim (Kallywood). Akwai wata’yar wasa da ta aro guda ]aya ta yini ahannunta to da ta mayar wa mai abinabinsa sai ta dawo tana }aryar wai ansace mata ita. Ka ji wayau, wai don kadaa gan ta gobe ba tare da ita ba. Da ma[anmaraya ya ce, “Kayan aro abinbanza ne, in mai abin ya kar~i abinsato dole za ka dawo naka.” Za ka yimamaki idan ka ga ’yar wasa rataye dajaka amma abin mamaki maimakon tasaka tarhon selulan a aljihu ko a jakasai ta ri}e shi a hannu, tana tafiya kanta}asa, tana danne-dannen banza da wofi.Ba ta ko gudu kada ]an aca~a yakwashe mata }afafu.

Wata yarinya kuma da na gani da itasai na ce “Ina kika samo ’yar rototuwa?”Sai ce min ta yi, “Mecece ’yar rototuwakuma?” Na amsa, “Wata ’yar na’uraryin surutai ce da ka]e-ka]e ke tasowacikinta idan an danna wa yaro, maganinkukan banza.” Yarinyar ta ce, “Kaibagidaje, duba ka gani, GSM ce, kuma

tawa ce ba ta aro ba ce!”Sai nake tambayar ta wanda ya sai

mata ko kuma nawa ta saya. Abin dakawai na tambaye ta shi ne, “To ga wasulambobi nan na gani a ciki rambatsau;wai na menene?” Ta amsa, “Ba phonenumbers ba ne, account number ]inane; yanzu na buga a banki suka fa]amin ko nawa ya rage daga cikinku]ina.” Ni kuwa dariya ta kama niamma sai na daure, na }ara jingina ajikin motar da ta same mu na har]e }afana ]an karkace kai.

Ba wani abu ne ya ba ni dariya ba saikawai don ta ce “yanzu na buga wayabanki.” Shin kun san wani abu? Alokacin da muke maganar an da]e dagama sallar magariba amma ba a yiisha’i ba. Kuma abin dariya wai yaroya tsinci ha}ori ranar Lahadi ce ba watarana ba. Da ma tun farkon shigowartaKano na yi ajiyar zuciya na ce to ’yan}arya kuma sai abin da ya }aru. Ai banda]e da yin maganar ba sai wani ]anfim ya sayi ]aya. Shi dai yana so a sanya saya kuma shi ba abin ya yi sanarwaa rediyo ko a mujalla ba don kowa yasani. Kun san abin da ya yi? Kawai idanya ga kuna mutunci ko kuma ya ]aukeka “mutum” sai ya ba ka aro. Kai kumaduk inda ka je da an ce ashe kai ma kasaya? Sai ka ce, “A’a, ta … ce”

Kafin shigowar selula a hannun ’yanfim yawancin kalmomin Turancin da zaka ri}a yawan ji su ne location, industry,shooting, still camera, editing, make-up,artist, recording, da sauransu. Yanzukuma abin ya }ara yawa domin wasukalmomin sun }ara shigowa, irin suGSM ]ina, mobile phone ]ina, handset,

landline, Nokia, da sauransuSai dai tun tafiya ba ta yi nisa ba har

sun fara cin karo da matsaloli dominkuwa na ji suna kuka da cewa “GSM isa great gamble.” Haka dai na ji wanifurodusa mai yawan yin Turanci yanafa]a wa wani babban jigo a harkar fim.Wasu kuma cewa suke yi, “Ana wahalarisar da sa}o daga handset zuwalandline.” Oho, ku dai kuka sanTurancin. Wata rana kuma wani yanazaune a mota na je na tsaya ina jira yagama danna tasa mu gaisa. Ya buga, yabuga bai ji an ]auka ba. Ya girgiza taya jijjiga ta, duk bai ji ]ililililin!]ililililin! ]ililililin! ba. Sai na ga yananeman kai ta ga bakinsa. Ko miyau zaitofa ya yi mata addu’a? Oho! Ina cemasa, “Barka da aiki!” sai ya yi zumburya fara magana: “... E, }warai kuwa! ...Na yi waya ]azun na ji shiru... To yanzudai zan tafi location, sai na dawo dayamma... Na gode...” Da ya gama yimin burga sai ya juyo yana yi min dariyawai shi ya buga waya daga inda yakebai je ofishin NITEL ba. Ni kuma da natabbatar burga ce, sai na ri}a yi masadariya. Dariyar darara kenan.

Ni dai ba ina yi wa ’yan fim bu}uluba ne don sun yi selula. Ci-gaba ne sukeyi. Kun san kwanan baya sun yi tserensaye ko sauya motoci (koda yake haryanzu ba su daina ba). To yanzu kotseren mallakar selula ake yi. Don ]anfim yana da mota bai da mobayil, baigama ‘ha]uwa’ ba kenan. Shi ko wandako motar ma bai yi ba, kaiconsa. Shi indai maganar ha]uwa ce, a gaskiya dasauransa.

Ya je ya sake lissafi kawai!

52

Kwanan nan aka yi wani abin mamaki, ban dariya, da takaici a Garin Kadoji. Wata sabuwar’yar wasa ce (Kyakkyawa) ta shigo harkar fim da kwantacce, ko kuma dai in ce ~oyayye.Kun san kwantacce? To, ita dai Kyakkyawa, nata cikin ba a san tana da shi ba, babu alama.Ta fito a finafinai ka]an, wasu ba a ko gama ]aukarsu ba, kuma akwai alamun za ta yiwasu. Na ji har wai furodusa Alhaji Malmo Rigimau yana kishinta, bai son kowa ya ra~eta, har da yi mata }aryar zai sa ta a wani fim ]insa can gaba. To, kwatsam, sai Kyakkyawata haifi namiji. A ranar ma furodusa Malam Wake yana jiranta ta zo Birnin Bayero sabodasu yi fim. Sai kawai ya samu waya ga abin da ya faru: wato ’yan Kadoji suna bi}i. Sai daiban binciko wanda ya yi cikin ba, tukuna (an ce wai na tsohon mijinta ne). Ku tambayiMalmo. Kai ko kyakkyawan jinjiri, Allah ya raya ka. Fagen shirin fim yana jiranka.

‘Kash! ta haifar musu ]a!’

Page 54: Mujallar FIM - March 2002

Fim, Maris 2002

Gagarabadau poster